Aminiya:
2025-03-25@14:28:12 GMT

Gwamnatin Yobe za ta gina gadar sama a kan N22.3bn

Published: 22nd, February 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Yobe, ta rattaba hannu kan kwangilar gina gadar sama da titin ƙarƙashin ƙasa a tsakiyar garin Damaturu, Babban Birnin Jihar, kan kuɗi Naira biliyan 22.3.

Wannan wani mataki ne na ci gaba a ƙoƙarin gwamnatin samar wa al’umma ababen more rayuwa.

Sanata Katung ya damu kan yadda wasu ta’azzara ta’addanci a kudancin Kaduna Zaɓen ƙananan hukumomin Osun na nan daram – Gwamna Adeleke

Kwamishinan ayyuka na jihar, Injiniya Umar Duddaye ne, ya sanya hannu a madadin gwamnati, yayin da Injiniya Habib Geojea ya wakilci kamfanin da zai aiwatar da aikin, Messrs Triacta Nigeria Limited.

Kwamishinan ya bayyana cewa gwamnatin Mai Mala Buni na bai wa manyan ayyukan ci gaba fifiko, wanda ya haɗa da tituna, gadoji, da magudanun ruwa.

Ya ce aikin gadar sama da ke shatale-shatalen Damaturu za a kammala shi cikin watanni 12.

Haka nan, an rattaba hannu kan kwangilar gina titin Damaturu zuwa Gambir tsakanin gwamnatin Yobe da kamfanin Messrs Elegance Construction Nigeria Limited, wanda za a kammala cikin watanni tara.

Kwamishinan ya ƙara da cewa ana shirin gina sabbin tituna masu tsawon kilomita 23.5 da magudanan ruwa masu nisan kilomita 27 a Damaturu, tare da sake da gyara titunan da ake buƙata.

Aikin zai shiga mataki na biyu a shekarar 2025.

Manajan yanki naTriacta Nigeria Limited ya tabbatar da cewa za su gudanar da aikin cikin inganci da wa’adin da aka tsara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gadar Sama

এছাড়াও পড়ুন:

Syria: SOHR ta fallasa jami’an tsaron sabuwar gwamnati na yi tsiraru kisan gilla

Kungiyar da ke sa ido da kare hakkin dan adam ta Syria (SOHR) ta fitar da fayafan bidiyo guda hudu da ke dauke da hotunan azabtarwa da kisa da jami’an tsaron sabuwar gwamnatin kasar  karkashin kungiyar Tahrir Sham  suke aiwatarwa a kan fararen hula tsiraru marasa rinjaye a kasar.

Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama a Syria ta bayyana a ranar Lahadi cewa, ta samu faifan bidiyo guda hudu ne da ke nuna yadda ake aiwatar da hukuncin kisa kan wasu matasa da ba sa dauke da makamai daga ‘yan Alawiyya, da jami’an tsaro suka aiwatar a kauyen al-Shir da ke yankin Latakia a ranar 7 ga watan Maris.

A cewar kungiyar, faifan bidiyon ya kara tabbatar da yadda aka aiwatar da kisan gillar da aka yi a yankunan gabar tekun Syria da kuma wadanda suka aikata hakan a kan fararen hula.

A cikin faifan bidiyo na farko ya nuna wasu matasa biyu sun durkusa a kasa yayin da jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria  suke zaginsu tare da lakada musu matsanancin duka, duk kuwa da ikirarin da suka yi na cewa ba su aikata wani laifi ba.

A cikin wani faifan bidiyo na biyu, an nuna yadda aka azabtar da wasu fararen hula hudu  ciki har da tsofaffi biyu, da kuma tilasta wa daya daga cikinsu sumbaci takalmin wani jami’in tsaro.

Kaset na uku ya nuna irin mumunan duka da aka yi wa fararen hula da bindigogi da karafa kafin daga baya kuma duk aka kashe su.

Dukkanin wadanda suka aikata wadannan munannan laifuka dai sabbin jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria ne da kungiyar Tahrir Sham mai dangantaka da kungiyar Alqaida ta kafa a Syria bayan hambarar da gwamnatin Bashar Assad.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren Gwamnati
  • Gwamna Uba Sani Ya Nada Sarkin Kauru Amirul Hajj Na Shekarar 2025
  • Fursunoni 12 sun tsere bayan fasa gidan yari a Kogi
  • Syria: SOHR ta fallasa jami’an tsaron sabuwar gwamnati na yi tsiraru kisan gilla
  • Dole Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Ta Daina Barazana Ga Masu Sukar Ta – Amnesty
  • Araghchi : Ya kamata Duniyar Musulmi ta dauki mataki mai karfi kan Isra’ila
  • Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
  • Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na Lallashi
  • Dalilan Gwamnatin Tarayya Na Zuba Naira Tiriliyan 1.5 A Bankin Aikin Noma -Kyari