Aminiya:
2025-04-19@19:23:09 GMT

Gwamnatin Yobe za ta gina gadar sama a kan N22.3bn

Published: 22nd, February 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Yobe, ta rattaba hannu kan kwangilar gina gadar sama da titin ƙarƙashin ƙasa a tsakiyar garin Damaturu, Babban Birnin Jihar, kan kuɗi Naira biliyan 22.3.

Wannan wani mataki ne na ci gaba a ƙoƙarin gwamnatin samar wa al’umma ababen more rayuwa.

Sanata Katung ya damu kan yadda wasu ta’azzara ta’addanci a kudancin Kaduna Zaɓen ƙananan hukumomin Osun na nan daram – Gwamna Adeleke

Kwamishinan ayyuka na jihar, Injiniya Umar Duddaye ne, ya sanya hannu a madadin gwamnati, yayin da Injiniya Habib Geojea ya wakilci kamfanin da zai aiwatar da aikin, Messrs Triacta Nigeria Limited.

Kwamishinan ya bayyana cewa gwamnatin Mai Mala Buni na bai wa manyan ayyukan ci gaba fifiko, wanda ya haɗa da tituna, gadoji, da magudanun ruwa.

Ya ce aikin gadar sama da ke shatale-shatalen Damaturu za a kammala shi cikin watanni 12.

Haka nan, an rattaba hannu kan kwangilar gina titin Damaturu zuwa Gambir tsakanin gwamnatin Yobe da kamfanin Messrs Elegance Construction Nigeria Limited, wanda za a kammala cikin watanni tara.

Kwamishinan ya ƙara da cewa ana shirin gina sabbin tituna masu tsawon kilomita 23.5 da magudanan ruwa masu nisan kilomita 27 a Damaturu, tare da sake da gyara titunan da ake buƙata.

Aikin zai shiga mataki na biyu a shekarar 2025.

Manajan yanki naTriacta Nigeria Limited ya tabbatar da cewa za su gudanar da aikin cikin inganci da wa’adin da aka tsara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gadar Sama

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta

Gwmanatin Sojin Nijar ta sanar da cewa sun sasanta da Gwmanatin Najeriya.

Hakan ta faru ne bayan ziyarar aiki da Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ya kai birnin Yamai, fadar gwamnatin Nijar.

Bayan sanya hannu kan takardar, Ministan Harkokin Wajen Nijar, Bakary You Sangare, ya bayyana cewa, “da ma Najeriya ’yan uwanmu ne, duk wanda ya ce zai raba  Nijar da Najeriya, shi da kansa ya san ba gaskiya ba ne, abu ne na Allah. Allah Ne Ya haɗa wannan zumunta ka, babu wanda ya isa ya raba ta.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
  • Neja Za Ta Kaddamar da Ayyukan Jiragen Sama Daga Filin Jirgin Sama na Bola Ahmed Tinubu.
  • Fani-Kayode ya zargi Isra’ila da Hannu a tashe-tashen hankula a Najeriya
  • Gwamnatin Yobe ta sayo hatsi don tunkarar kakar bana
  • ISWAP sun ruguza gadar Mandafuma babbar hanya a Borno
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Siyawa ‘Yan Gudun Hijira Gidan Miliyan 100
  • Gazawar Gwamnatin Tinubu Ce Ke Haddasa Zubar Da Jini A Filato – Ƙungiyar Dattawan Arewa
  • AGILE: Gwamnatin Kaduna da Bankin Duniya Na Sauya Rayuwar ’Ya’ya Mata Ta Hanyar Ilimi
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar sun sasanta
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta