Shugabannin Kasashen Larabawa Sun Tattauna Kan Batun Gaza Da Yankin
Published: 22nd, February 2025 GMT
Shugabannin kasashen Larabawa sun tattauna kan batun Gaza dama halin da ake ciki yankin.
Bisa gayyatar Yarima mai jiran gado na Saudiyya Mohammed bin Salman, an gudanar da taron ‘yan uwantaka na yau da kullun a birnin Riyadh a ranar Juma’a inji kamfanion dilancin labaren kasar na SPA.
Taron ya samu halartar sarki Abdullah II na Jordan, da sarkin Qatar Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani, da shugaban kasar Masar, da Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani, na kasar Hadaddiyar Daular Larabawa hyan, da Sarkin Kuwait Sheikh Meshal Al-Ahmad Al-Jaber Al-Sabah, da kuma Yarima mai jiran gado kuma firaministan kasar Bahrain Yarima Salman bin Hamad Al Khalifa.
Taron ya ba da damar tuntubar juna kan batutuwa daban-daban na shiyya-shiyya da na kasa da kasa, tare da mai da hankali musamman kan kokarin hadin gwiwa na goyon bayan al’ummar Falastinu da kuma mayar da martani kan abubuwan da ke faruwa a zirin Gaza.
Shugabannin sun yi maraba da gudanar da taron gaggawa na kasashen Larabawa da aka shirya gudanarwa a birnin Alkahira na Masar a ranar 4 ga watan Maris, mai zuwa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Karfafa Gwiwar Kamfanonin Kasashen Duniya Da Su Fadada Zuba Jari A Sin
Mataimakin firaministan kasar Sin He Lifeng ya bayyana a jiya Lahadi cewa, kasar Sin za ta ci gaba da bude kofa ga kasashen waje, kuma tana maraba da kamfanonin kasashen duniya da su fadada zuba jari a kasar Sin, domin zurfafa samun moriyar juna da samun nasara tare.
He ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ya yi da shugabannin manyan kamfanoni na duniya a nan birnin Beijing, yayin da suka yi musayar ra’ayi kan yanayin tattalin arzikin duniya da na kasar Sin, da hadin gwiwar Sin da Amurka a fannin tattalin arziki da cinikayya, da fadada zuba jari a kasar Sin.
He ya ce, tattalin arzikin kasar Sin yana da karfin juriya, da fa’ida mai yawa, da wadataccen kuzari, ya kara da cewa, kasar Sin ta kuduri aniyar samun ci gaba mai inganci, da fadada bude kofa ga kasashen waje a babban mataki, da ci gaba da kyautata yanayin kasuwanci, tare da maraba da kara zuba jari da kamfanonin kasa da kasa suke yi a kasar Sin, don cin gajiyar damammakin da ke tattare da ci gaban kasar.
Shugabannin harkokin kasuwanci na kamfanoni na kasa da kasa da suka halarci wannan taro sun bayyana cewa, suna dora muhimmanci kan kasuwar kasar Sin, kuma suna da kwarin gwiwa game da makomar tattalin arzikin kasar Sin, kana sun bayyana aniyarsu ta yin hadin gwiwa na dogon lokaci tare da kasar Sin. (Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp