HausaTv:
2025-03-25@19:50:56 GMT

Tawagogi Na Isa Lebanon Domin Halartar Jana’izar Sayyed Hassan Nasrallah

Published: 22nd, February 2025 GMT

Tawagogi na ci gaba da isa Beirut, domin halartar jana’izar tsohon sakataren kungiyar Hezbollah ta Lebanon mirigayi Sayyid Hassan Narsrallah.

Iran, ma ta sanar da aikewa da wata babbar tawaga zuwa kasar ta Lebanon domin halartar jana’izar shahiddan Sayyid Hasan Nasrallah da Sayyed Hashem Safieddine.

A gobe Lahadi ne za a gudanar da jana’izar wadannan shahidai biyu a birnin Beirut, inda ake sa ran tawagogin daga kasashe 78 za su halarta.

Shugaban kwamitin da ke sa ido a jana’izar, Sheikh Ali Daher, ya sanar a ranar Juma’a cewa za a fara jana’izar a hukumance a ranar Lahadi daga karfe 1 na rana (agogon kasar).

Jami’ai da dama da suka hada da shugaban kasar Lebanon da kakakin majalisar dokokin kasar za su halarci jana’izar, ya kuma kara da cewa wata babbar tawaga ta Iran za ta halarci bikin ba tare da yin karin bayani ba.

Bugu da kari, Sheikh Naim Qassem babban sakataren kungiyar Hizbullah zai gabatar da jawabi a wajen bikin.

Idan dai ba a manta ba Sayyid Nasrallah ya yi shahada ne a wani harin bam na Isra’ila a kudancin birnin Beirut a ranar 27 ga watan Satumban 2024.

A nasa bangaren, Sayyed Safieddine ya yi shahada ne a wani harin da Isra’ila ta kai a watan Oktoban 2024.

Kungiyar Hizbullah ta zabi dage bikin jana’izar mutanen biyu, saboda hadarin halin da ake ciki na iya fuskantar hare-haren hare-haren Isra’ila.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Lauyoyi 77 a Jamus sun yi kira ga gwamnati da ta mutunta sammacin ICC na cafke Netanyahu

Wasu lauyoyi 77 a Jamus sun bukaci gwamnatin kasar da ta mutunta sammacin kotun hukunta manya laifuka ta duniya ICC, na cafke firaministan Isra’ila Banjamin Netanyahu.

 A cikin wata sanarwar hadin gwiwa da da suka fitar, fitattun lauyoyin 77 sun kuma bayyana yiwuwar kasancewar Netanyahu a Jamus a matsayin take doka da kuma hakkin kasar.

Lauyoyin sun soki Friedrich Martin Josef Merz, dan siyasa kuma shugaban gwamnati a nan gaba, saboda sanarwar da ya yi a lokacin yakin neman zabe cewa zai samo hanyar gayyatar firaministan Isra’ila da kuma tattaunawa ta wayar tarho da Netanyahu bayan nasararsa.

Lauyoyin sun kuma yi Allah wadai da halin wasu jami’o’in da suka soke jawabin da Francesca Albanese mai kula da harkokin kare hakkin bil’adama ta Majalisar Dinkin Duniya ta yi a yankin Falasdinu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI
  • ECOWAS Za Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • Hamas : Isra’ila ta yi amfani da sulhu wajen tattara bayanai kan shugabannin Hamas domin kashe su
  • Lauyoyi 77 a Jamus sun yi kira ga gwamnati da ta mutunta sammacin ICC na cafke Netanyahu
  • Ukraine: Tawagogin Rasha da Amurka sun kammala tattaunawa a Saudiyya
  • Dakarun Yemen sun kara kai hare-hare goyan bayan Falasdinu
  • Isra’ila ta kashe Falasdinawa 61 cikin sa’o’i 24
  •  Shugaban Majalisar Dokokin Lebanon Ya Yi Gargadi Akan Masu Tunanin Kulla Alakar Kasar Da HKI
  • Iran ta yi gargadin cewa keta hurumin Lebanon da Isra’ila ke yi barazana ne ga zaman lafiyar duniya
  • Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya