Iran Ta Kudiri Anniyar Karfafa Alakarta Da Kasashen Afirka
Published: 22nd, February 2025 GMT
Iran ta jadadda anniyarta ta karfafa alaka da kasashen Afrika, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen kasar ta tabbatar.
A cikin wani sako da ya aike ta shafin X a ranar Juma’a, kakakin ma’aikatar, Esmaeil Baghaei, ya yi tsokaci kan ganawar da aka yi a ranar Alhamis tsakanin mataimakin shugaban kasar na farko Mohammad Reza Aref da jakadun kasashen Afirka a Tehran.
Baghaei ya bayyana cewa, taron ya nuna aniyar Iran na karfafa alaka da fadada hadin gwiwa da kasashen Afirka a fannoni daban-daban na moriyar juna.
A yayin ganawar, Aref ya bayyana cewa, dabarun gwamnatin Iran, karkashin shugaba Masoud Pezeshkian, ya yi daidai da ainihin manufofin Iran na inganta alaka da kasashen Afirka.
Ya jaddada manufar karfafa hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu, a bangarori da dama, da kuma shiyya-shiyya.
“Idan aka yi la’akari da irin karfin da muke da shi, ta hanyar hada kai da hada albarkatunmu, za mu iya ba da gudummawa sosai ga ci gaban dangantaka da kuma yi wa jama’armu hidima,” in ji Aref.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran da UAE sun kirayi Isra’ila da Amurka da su kawo karshen hare-harensu a Gaza da Yemen
Kasashen Iran da Hadaddiyar Daular Larabawa sun bayyana matukar damuwarsu kan yadda gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta sake dawo da yakin kisan kare dangi a zirin Gaza da kuma hare-haren da Amurka ke kaiwa kasar Yemen.
A wata tattaunawa ta wayar tarho a wannan Juma’a, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da takwaransa na UAE Abdullah bin Zayed Al Nahyan, sun tattauna batutuwan da suka shafi yankin, musamman ma ayyukan wuce gona da iri na Isra’ila a Gaza da kuma hare-haren Amurka a Yemen.
Araghchi ya yi kakkausar suka kan kisan gillar da gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta yi wa daruruwan Falasdinawa da ba su ji ba ba su gani ba tun daga ranar Talata, yana mai jaddada cewa yin hakan saba yarjejeniyar tsagaita bude wuta ne da aka rattaba hannu a kansa.
Ya kuma yi Allah wadai da hare-haren da sojojin Amurka ke ci gaba da kai wa kasar Yemen, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mata da kananan yara da dama, tare da lalata muhimman ababen more rayuwa na yankin, da kuma jefa mutane cikin kangin talauci da yunwa.
Araghchi ya kara da cewa, laifuffukan da gwamnatin yahudawan sahyoniya ke aikatawa a Gaza da kuma harin da Amurka ta kai kan kasar Yaman na bukatar daukar matakin gaggawa da hadin gwiwa daga kasashen yankin da kum akasashen musulmi, domin dakatar da wannan ta’addanci da ke ci gaba da kawo rashin tsaro a duk fadin yankin gabas ta tsakiya.
A nasa bangaren, Ministan kasar UAE Abdullah bin Zayed ya bayyana matukar damuwarsa kan tabarbarewar al’amura a yankin, yana mai bayyana lamarin a matsayin abin damuwa matuka.
Ya jaddada bukatar ci gaba da tuntubar juna tsakanin kasashen yankin domin hana ci gaba da tabarbarewar zaman lafiya.
Rahotanni sun tabbatar da cewa sojojin Isra’ila sun zafafa kai hare-hare ta sama da kuma ta kasa a zirin Gaza tun daga ranar Talata, inda suke kai hari kan wuraren zaman jama’a da hakan ya hada da wuraren da aka tsugunnar da dubban mutane da suka rasa muhallansu da kuma gidaje, gami da asibitoci, tare da hana duk wasu ayyuka na jin kai ko ceton jama’a ko kai daukin gaggawa.