Iran Ta Kudiri Anniyar Karfafa Alakarta Da Kasashen Afirka
Published: 22nd, February 2025 GMT
Iran ta jadadda anniyarta ta karfafa alaka da kasashen Afrika, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen kasar ta tabbatar.
A cikin wani sako da ya aike ta shafin X a ranar Juma’a, kakakin ma’aikatar, Esmaeil Baghaei, ya yi tsokaci kan ganawar da aka yi a ranar Alhamis tsakanin mataimakin shugaban kasar na farko Mohammad Reza Aref da jakadun kasashen Afirka a Tehran.
Baghaei ya bayyana cewa, taron ya nuna aniyar Iran na karfafa alaka da fadada hadin gwiwa da kasashen Afirka a fannoni daban-daban na moriyar juna.
A yayin ganawar, Aref ya bayyana cewa, dabarun gwamnatin Iran, karkashin shugaba Masoud Pezeshkian, ya yi daidai da ainihin manufofin Iran na inganta alaka da kasashen Afirka.
Ya jaddada manufar karfafa hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu, a bangarori da dama, da kuma shiyya-shiyya.
“Idan aka yi la’akari da irin karfin da muke da shi, ta hanyar hada kai da hada albarkatunmu, za mu iya ba da gudummawa sosai ga ci gaban dangantaka da kuma yi wa jama’armu hidima,” in ji Aref.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Wang Yi Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Uganda
Ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya gana da takwaransa na kasar Uganda Jeje Odongo a cibiyar MDD da ke birnin New York.
Yayin ganawar a ranar 18 ga wata, Wang Yi ya bayyana cewa, ana bukatar ra’ayin Afirka yayin da ake yada ra’ayin bangarori daban daban da kuma daidaita harkokin duniya baki daya. Ya ce kasar Sin tana son hada hannu da kasashen Afirka wajen kafa tsarin daidaita harkokin duniya mai adalci da kuma samar da gudummawa wajen shimfida zaman lafiya da samun ci gaba a duniya. Wang Yi ya ce Sin tana yabawa kasar Uganda bisa muhimmiyar rawar da ta taka yayin da take shugabantar kungiyar kasashe ‘yan ba ruwanmu wato NAM, da taya ta murnar zama kasar da ta hada kan kasashen BRICS, haka kuma, Sin tana son yin kokari tare da kasar Uganda wajen sa kaimi ga hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa da tabbatar da adalci a duniya baki daya.
A nasa bangare, minista Odongo ya amince da tunanin girmama juna da tabbatar da ikon mallakar kasa da zaman daidaito da kuma adalci da kasar Sin da sauran kasashen BRICS suke bi, yana mai cewa kasarsa tana son yin kokari tare da kasashen BRICS da shiga bangare mai dacewa a duniya. (Zainab Zhang)