Aminiya:
2025-04-14@18:24:37 GMT

Dalilan ƙara kuɗin Jami’ar Gombe — Gwamna Inuwa

Published: 22nd, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana cewa ƙarin kuɗin makarantar Jami’ar Jihar Gombe (GSU) da kashi 120 cikin 100 ya zama dole domin tabbatar da ɗorewar ingancin ilimi a jami’ar.

Gwamnan ya bayyana haka ne yayin rantsar da kwamitocin gudanarwa na manyan makarantu da hukumomin gwamnati, inda ya jaddada cewa kuɗaɗen makaranta na GSU sun yi ƙasa sosai idan aka kwatanta da na sauran jami’o’in jihohin makwabta kamar Borno, Adamawa, da Bauchi.

Gwamnatin Yobe za ta gina gadar sama a kan N22.3bn Wasu sassan Abuja za su kasance cikin duhu a ƙarshen mako – TCN

“Muna mayar da hankali sosai kan ilimin firamare da sakandare, amma ilimin manyan makarantu yana da tsada sosai kuma yana buƙatar zuba jari mai tsoka.

“Ƙarin kuɗin da muka yi zai bai wa jami’ar damar ci gaba da bayar da ilimi mai nagarta,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa ƙarin kuɗin makarantar ya samu ne bisa buƙatun ƙungiyar malaman jami’o’i (ASUU) da sauran ƙungiyoyi, domin ƙara kuɗaɗen shiga don inganta jami’ar.

Gwamnan ya buƙaci ɗalibai da iyayensu su yi amfani da shirin lamunin ɗalibai na Gwamnatin Tarayya don samun sauƙin biyan kuɗaɗen makaranta.

“Haƙiƙa, ilimi ba asara ba ne. Ku nemi lamunin ɗalibai domin ku samu damar yin karatu, wanda zai taimaka wa jami’a ta bunƙasa,” in ji Yahaya.

Ya bayyana cewa Gwamnatin Jihar Gombe na bayar da goyon baya sama da sauran jihohi, amma har yanzu akwai buƙatar jami’ar ta nemo wasu hanyoyin samun kuɗaɗe domin tabbatar da ɗorewar ayyukanta da gogayya da sauran manyan makarantu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibai Gwamna Inuwa Jami ar Jihar Gombe Kuɗin Makaranta

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano

Shugaban Kasa Bola Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran babban titin Abuja-Kaduna-Zariya-Kano, wadda ke da matukar muhimmanci ga tattalin arzikin Arewacin Najeriya.

Da yake jawabi a taron kaddamarwar a Kagarko, Jihar Kaduna, Gwamna Uba Sani, ya bayyana yadda aka yi watsi da hanyar da kuma irin mummunan tasirin da hakan ya yi ga rayuka da ci-gaban tattalin arziki.

Gwamna Uba Sani, ya yaba wa Tinubu bisa farfado da aikin, yana mai nuni da muhimmancin hanyar a matsayinta na mafi yawan zirga-zirgar ababen hawa a Arewa.

Da yake ba da tabbacin kamma aikin a cikin watanni 14, Tinubu wanda Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi, ya ce za a gina titin ne da kankare, kamar babbar hanyar Legas zuwa Kalaba.

An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu

Ministan ya kara da cewa aikin zan dangana har zuwa filin jirgin sama na Kano, kuma za a sanya kyamarorin CCTV gaba daya a tsawon titin, wanda sabon dan kwangila ne zai aiwatar.

Ya ce, shugaban kasa ya amince da naira biliyan 252 don muhimman sassan aikin, inda aka riga aka biya kashi 30%, yanan mai yaba muhimmiyar rawar da Gwamna Uba Sani ya taka a aikin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Aljeriya ta yi barazanar korar jami’an diflomasiyyar Faransa 12
  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • Inganta Rayuwar Al’umma: Amurka Da Ƙungiyar Kasuwanci Ta Nijeriya Sun Karrama Gwamna Lawal
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • Mutum ɗaya ya mutu a faɗan ƙungiyar asiri a Maiduguri
  • Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma
  • Kashe-kashen Filato: Jami’an tsaro na sassauta wa masu laifi —Tsohon gwamnan soji