Fira ministan gwamnatin mamayar Isra’ila ya ba da umarnin tsananta kai hare-hare kan yankunan yammacin gabar kogin Jordan biyo bayan hare-haren bama-bamai da aka kai a birnin Tel Aviv

Fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu ya bada umarnin kai hare-haren wuce gona da iri kan sansanin ‘yan gudun hijira na Tulkaram da ke arewacin gabar yammacin kogin Jordan a jiya Juma’a.

Yanzu kusan wata guda ke nan da Netanyahu ya ba da umarnin tsananta hare-haren kan sansanin ‘yan gudun hijiran na Tulkram, kamar yadda ofishinsa ya bayyana, kwana guda bayan tashin bama-bamai kan motocin bus-bus a yankin Bat Yam da ke kudancin birnin Tel Aviv fadar mulkin haramtacciyar kasar Isra’ila.

Ofishin fira ministan ya bayyana cewa: Kwanan nan ne Netanyahu ya ziyarci sansanin ‘yan gudun hijira na Tulkaram” inda ya ba da umarnin kara kai hare-haren wuce gona da iri kan yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wang Yi Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Uganda

Ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya gana da takwaransa na kasar Uganda Jeje Odongo a cibiyar MDD da ke birnin New York.

Yayin ganawar a ranar 18 ga wata, Wang Yi ya bayyana cewa, ana bukatar ra’ayin Afirka yayin da ake yada ra’ayin bangarori daban daban da kuma daidaita harkokin duniya baki daya. Ya ce kasar Sin tana son hada hannu da kasashen Afirka wajen kafa tsarin daidaita harkokin duniya mai adalci da kuma samar da gudummawa wajen shimfida zaman lafiya da samun ci gaba a duniya. Wang Yi ya ce Sin tana yabawa kasar Uganda bisa muhimmiyar rawar da ta taka yayin da take shugabantar kungiyar kasashe ‘yan ba ruwanmu wato NAM, da taya ta murnar zama kasar da ta hada kan kasashen BRICS, haka kuma, Sin tana son yin kokari tare da kasar Uganda wajen sa kaimi ga hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa da tabbatar da adalci a duniya baki daya.

A nasa bangare, minista Odongo ya amince da tunanin girmama juna da tabbatar da ikon mallakar kasa da zaman daidaito da kuma adalci da kasar Sin da sauran kasashen BRICS suke bi, yana mai cewa kasarsa tana son yin kokari tare da kasashen BRICS da shiga bangare mai dacewa a duniya. (Zainab Zhang)

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Wani Mutum Tare Da Sace Mutum Biyu A Kaduna
  • Wang Yi: Sin Za Ta Ci Gaba Da Mara Baya Ga Garambawul Na Kungiyar WTO 
  • Sojojin Ruwa Da Kuma Sojijin Sama Na JMI Sun Hada Guiwa Don Yin atisaye Tare Mai taken Zulfikar
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Sun Jaddada Cewa: Zasu Kai Harin Daukan Fansa Na Alkawarin Gaskiya Kan Isra’ila
  • Kungiyar Hizbullah Ta Lebanon Ta Jaddada Rashin Amincewarta Da Mika Kan Kasar Ga Amurka Da Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Sojojin Faransa Sun Mika Sansanin Soji Mafi Girma Da Suka Mamaye Ga Sojojin Faransa
  • Wasu Motocin Bas-Bas Sun Tarwatse A Haramtacciyar Kasar Isra’ila A Yankin Bat Yam A Kudancin Tel-Aviv
  • Wang Yi Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Uganda
  • Gwamnatin Kano Ta Amince da  Kashe Naira Biliyan 33.4 Don Ayyukan Ci Gaba