Fira ministan gwamnatin mamayar Isra’ila ya ba da umarnin tsananta kai hare-hare kan yankunan yammacin gabar kogin Jordan biyo bayan hare-haren bama-bamai da aka kai a birnin Tel Aviv

Fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu ya bada umarnin kai hare-haren wuce gona da iri kan sansanin ‘yan gudun hijira na Tulkaram da ke arewacin gabar yammacin kogin Jordan a jiya Juma’a.

Yanzu kusan wata guda ke nan da Netanyahu ya ba da umarnin tsananta hare-haren kan sansanin ‘yan gudun hijiran na Tulkram, kamar yadda ofishinsa ya bayyana, kwana guda bayan tashin bama-bamai kan motocin bus-bus a yankin Bat Yam da ke kudancin birnin Tel Aviv fadar mulkin haramtacciyar kasar Isra’ila.

Ofishin fira ministan ya bayyana cewa: Kwanan nan ne Netanyahu ya ziyarci sansanin ‘yan gudun hijira na Tulkaram” inda ya ba da umarnin kara kai hare-haren wuce gona da iri kan yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sudan: Sojoji na ci gaba karbe mahimman gine-gine a birnin Khartoum

A Sudan bayan sake karbe fadar shugaban kasa da ke birnin Khartoum, sojojin kasar sun ci gaba da kai farmaki a babban birnin kasar a ranar Asabar, inda suka sake karbe iko da wasu gine-gine, ciki har da babban bankin kasa da hedkwatar hukumar leken asiri da kuma gidan adana kayan tarihi na kasar.

Ana kallon wannan a matsayin nasarorin ga Janar al-Burhan a babban birnin kasar, wanda rikicin cikin gida ya rutsa da shi na tsawon shekaru biyu.

A wannan Asabar, kakakin rundunar sojojin kasar, Janar Nabil Abdullah, ya sanar a cikin wata sanarwa cewa sojojin na ci gaba da samun nasara a birnin Khartoum, Ya kuma ce sojojin sun “kore daruruwan ‘yan bindiga.

A sa’i daya kuma, ana ci gaba da gwabza fada a yankin Darfur, wanda kusan yana karkashin ikon dakarun RSF.

A cewar masu fafutukar kare hakkin jama’a, akalla fararen hula 45 ne aka kashe a ranar Alhamis a wani harin da dakarun sa kai suka kai a garin Al-Malha da ke arewacin Darfur.

Sojojin sun yi ikirarin cewa sun yi wa garin kawanya tare da kashe makiya sama da 380.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lauyoyi 77 a Jamus sun yi kira ga gwamnati da ta mutunta sammacin ICC na cafke Netanyahu
  • An Ɗauko Sojoji Daga Waje Don Horas Da Dakarun Nijeriya 
  • An Ɗauko Sojoji Daga Wajen Don Horas Da Dakarun Nijeriya 
  •  Syria: Isra’ila Ta Kai Hari A Kan Sansanin Soja A Yankin Dar’a
  • Iran ta yi gargadin cewa keta hurumin Lebanon da Isra’ila ke yi barazana ne ga zaman lafiyar duniya
  • Duniya na ci gaba da yin tir da Isra’ila kan dawo da hare-harenta a Gaza
  • Araghchi : Ya kamata Duniyar Musulmi ta dauki mataki mai karfi kan Isra’ila
  • Sudan: Sojoji na ci gaba karbe mahimman gine-gine a birnin Khartoum
  • Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
  •  Haaretz: Sojojin Isra’ila Suna Kan Shirya Kai Wa Gaza Hari Ta Kasa