Leadership News Hausa:
2025-03-25@03:22:33 GMT

Gwamna Adeleke Ya Kaɗa Ƙuri’a a Zaɓen Ƙananan Hukumomin Osun

Published: 22nd, February 2025 GMT

Gwamna Adeleke Ya Kaɗa Ƙuri’a a Zaɓen Ƙananan Hukumomin Osun

Gwamnan Jihar Osun, Sanata Ademola Adeleke, ya kaɗa ƙuri’arsa a zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a faɗin jihar a ranar Asabar. Gwamnan ya isa rumfar zaɓensa da ke Sagba/Abogunde, Ƙaramar Hukumar Ede, inda aka tantance shi kafin ya kaɗa kuri’arsa.

Zaɓen, wanda ake gudanarwa don zaɓen sabbin shugabanni a ƙananan hukumomi 30 na jihar, ya samu fitowar masu zaɓe sosai tare da ingantaccen tsaro.

Gwamna Adeleke ya yaba da yadda zaɓen ke tafiya cikin lumana, inda ya buƙaci al’umma su ci gaba da kaɗa ƙuri’a ba tare da tsoro ko matsin lamba ba.

Gwamnan Shekarar 2024: Sanata Ademola Jackson Nurudeen Adeleke An Yanke Wa Mutane 5 Hukuncin Kisa Bayan Sun Kashe Wani Bafullatani A Jihar Osun

Da yake jawabi ga manema labarai bayan kaɗa ƙuri’arsa, ya jinjinawa hukumar zaɓe ta Jihar Osun (OSSIEC) bisa shirya ingantaccen zaɓe. Ya kuma jaddada muhimmancin dimokuraɗiyya a matakin ƙananan hukumomi, yana mai kira ga ‘yan jihar da su fito kwansu da kwarkwata domin amfani da hakkinsu na zaɓe.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ribas: Ba mu karɓi sisin kwabo domin amincewa da dokar ta baci ba – Majalisar Wakilai

Majalisar wakilai ta tarayya ta yi watsi da zargin da ake yi ga ‘yan majalisar tarayya na cin hanci da rashawa domin marawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu baya na ayyana dokar ta baci a jihar Ribas.

Dan majalisa mai wakiltar mazabar Gwaram daga jihar Jigawa, Honarabul Yusuf Shittu Galambi, ne ya kare majalisar a yayin da ake ta cece-kuce kan batun kafa dokar ta-baci a jihar Ribas, inda wasu kungiyoyi ke zargin majalisar dokokin kasar da yin kasa a gwiwa wajen yanke hukunci.

Sai dai, Galambi a wata sanarwa da ya fitar a yau Asabar, ya ce babu gaskiya a ikirarin na cewa an tursasa ‘yan majalisar kan matakin da shugaban kasar ya dauka.

A cewarsa, yawancin mambobin sun goyi bayan matakin ne saboda ceto dimokuradiyya da kare muradun al’ummar jihar Ribas.

Dattawan Arewa sun buƙaci Tinubu ya dawo da Fubara kan kujerarsa

Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia

Dan majalisar ya bayyana cewa majalisar ta yanke shawarar ne bisa son tabbatar da kishin kasa, hadin kan siyasa, zaman lafiya, da kare dimokuradiyya.

“Na yi mamakin yadda kafafen yada labarai suka rika yada labaran karya, musamman kan zargin da ake yi mana, cewa mun an tilasta mana mu zartar da kudurin goyon bayan matakin da shugaban kasa ya dauka a jihar Ribas da kuma karbar daloli”

“Ya kamata ‘yan Najeriya su yaba da rawar da ‘yan majalisar dokokin kasar ke takawa wajen neman shugaban kasa ya kafa wata tawagar sasanta yan siyasa kafin karewar wa’adin dokar ta-baci na watanni shida.

Ya kuma jaddada cewa dole ne a kare dimokradiyya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Cafke Mutum 2 Kan Zargin Kashe Ɗan Achaɓa Da Sace Babur Ɗinsa A Bauchi 
  • Gwamna Uba Sani Ya Nada Sarkin Kauru Amirul Hajj Na Shekarar 2025
  • Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya
  • Gobara ta tashi a gidan mai sakamakon fashewar tanka a Neja
  • Gwamnonin Arewa sun yi wa Radda ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsa
  • Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
  • Dakatar da Gwamnan Ribas zubar da ƙimar Nijeriya ne a idon duniya — Jonathan
  • Ribas: Ba mu karɓi sisin kwabo domin amincewa da dokar ta baci ba – Majalisar Wakilai
  • Dattawan Arewa sun buƙaci Tinubu ya dawo da Fubara kan kujerarsa