Aminiya:
2025-02-22@22:12:29 GMT

Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kano ta raba kayan tallafi

Published: 22nd, February 2025 GMT

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Kano (SEMA) da Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), sun fara raba kayayyakin tallafi ga mutum 507 da ambaliyar ruwa ta shafa a jihar a 2024.

An gudanar da rabon kayayyakin a ranar Juma’a a Ƙananan Hukumomin Kibiya da Madobi, inda Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya miƙa kayayyakin ga waɗanda suka ci gajiyar shirin.

Ɗan Abacha ya kare mahaifinsa bayan ƙaddamar da littafin IBB Sibil Difens ta cafke mutum 17 kan aikata sata a Yobe

Kwamishinan Harkokin Jin-ƙai da Rage Talauci, Alhaji Adamu Aliyu Kibiya ne, ya wakilci gwamnan.

Gwamnan, ya gode wa NEMA bisa goyon bayan da ta ke bai wa jihar, tare da yaba wa SEMA saboda jajircewarta wajen tabbatar da cewa tallafin ya isa ga waɗanda abin ya shafa.

“Muna da niyyar ci gaba da aiki tare da hukumomin da suka dace don inganta shirye-shiryen daƙile iftila’i a Kano,” in ji shi.

“Gwamnati za ta ci gaba da ƙarfafa haɗin gwiwa don kare lafiyar jama’a.”

Daraktar Janar na NEMA, Hajiya Zubaida Umar, ta ce wannan tallafi wani ɓangare ne na ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya na taimaka wa waɗanda ambaliya ta shafa.

Ta hannun Kwamandan NEMA a Kano, Dokta Nura Abdullahi, ta bayyana cewa an amince da tallafin ne bayan Gwamnatin Tarayya ta karɓi rahoto kan ɓarnar da ambaliyar ta haifar.

“Gwamnatin Tarayya tana jajanta musu kan yanayin da suka shiga,” in ji ta.

Kayayyakin da aka raba sun haɗa da buhu 500 na shinkafa mai nauyin kilo 25, buhu 500 na masara mai nauyin kilo 25, katan 45 na tumatirin gwangwani, katan 45 na man girki, katan 45 na maggi, da buhu 20 na gishiri.

Sakataren Zartarwa na SEMA, Alhaji Isyaku Kubarachi, ya buƙaci waɗanda suka amfana da su yi amfani da kayayyakin yadda ya dace.

Wani daga cikin waɗanda suka ci gajiyar shirin, Nura Sani, ya nuna jin dadinsa.

“Wannan tallafi zai taimaka mana sosai a wannan mawuyacin lokaci. Muna godiya ga gwamnati bisa ƙoƙarinta,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Haɗarin mota ya laƙume rayuka 12 a Neja

Aƙalla mutum 12 — ciki har da mata huɗu da maza takwas — sun riga mu gidan gaskiya a sanadiyyar wani mummunan haɗarin mota da ya auku a kan hanyar Lapai zuwa Agaie da ke Jihar Neja.

Wani da lamarin na safiyar wannan Asabar ɗin ya faru a kan idonsa, ya shaida wa Aminiya cewa uku daga cikin matan da suka rasu ’yan gida ɗaya ne.

Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kano ta raba kayan tallafi Ɗan Abacha ya kare mahaifinsa bayan ƙaddamar da littafin IBB

Sai dai wasu fasinjoji uku da suka haɗa da mata biyu da direban motar sun tsallake rijiya da baya, inda a yanzu suke samun kulawa a Babban Asibitin Lapai.

Bayanai sun ce haɗarin ya auku ne bayan wata taho-mu-gama da aka yi tsakanin wata mota ƙirar bas ɗauke da fasinjoji 15 da kuma wata tirela a daidai ƙauyen Nami.

Da yake zantawa da Aminiya ta wayar tarho, direban motar, Mohammed Baba, ya ce lamarin ya auku ne a yayin da suke kan hanyar tafiya Ƙaramar Hukumar Katcha bayan sun taso daga tashar mota ta Kasuwar Gwari da ke birnin Minna.

Direban ya alaƙanta haɗarin da tsautsayi wanda ya ce ya auku ne yayin da direban tirelan ya yi yunƙurin ƙetare wata mota da ke gabansa, lamarin da ya janyo motocin suka yi karo da juna.

Sai dai ya ce tuni direban tirelan ya arce da bayan faruwar lamarin.

Kwamandan Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa FRSC shiyyar Neja, Kumar Tsukwam, ya tabbatar da faruwar lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Ruwa Da Kuma Sojijin Sama Na JMI Sun Hada Guiwa Don Yin atisaye Tare Mai taken Zulfikar
  • Haɗarin mota ya laƙume rayuka 12 a Neja
  • Gwamnatin Yobe za ta gina gadar sama a kan N22.3bn
  • Karyewar Farashi: Ba mu shigo da kayan abinci daga waje ba — Minista
  • Kayan Abinci: Gwamnatin Nijeriya Ta Buƙaci ‘Yan Kasuwa Su Rage Farashi
  • Shirin Rigakafin Cututtuka Na UNICEF/GAVI Ya Sami Cikakken Hadin Kan Gwamnatin Jihar Jigawa
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 12, sun sace wasu a Zariya
  • Gwamnatin Kano Ta Amince da  Kashe Naira Biliyan 33.4 Don Ayyukan Ci Gaba
  • NAJERIYA A YAU: Tanadin Dokar Kasa Kan Kirkirar Gwamnatin Bibiya A Kano