Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kano ta raba kayan tallafi
Published: 22nd, February 2025 GMT
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Kano (SEMA) da Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), sun fara raba kayayyakin tallafi ga mutum 507 da ambaliyar ruwa ta shafa a jihar a 2024.
An gudanar da rabon kayayyakin a ranar Juma’a a Ƙananan Hukumomin Kibiya da Madobi, inda Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya miƙa kayayyakin ga waɗanda suka ci gajiyar shirin.
Kwamishinan Harkokin Jin-ƙai da Rage Talauci, Alhaji Adamu Aliyu Kibiya ne, ya wakilci gwamnan.
Gwamnan, ya gode wa NEMA bisa goyon bayan da ta ke bai wa jihar, tare da yaba wa SEMA saboda jajircewarta wajen tabbatar da cewa tallafin ya isa ga waɗanda abin ya shafa.
“Muna da niyyar ci gaba da aiki tare da hukumomin da suka dace don inganta shirye-shiryen daƙile iftila’i a Kano,” in ji shi.
“Gwamnati za ta ci gaba da ƙarfafa haɗin gwiwa don kare lafiyar jama’a.”
Daraktar Janar na NEMA, Hajiya Zubaida Umar, ta ce wannan tallafi wani ɓangare ne na ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya na taimaka wa waɗanda ambaliya ta shafa.
Ta hannun Kwamandan NEMA a Kano, Dokta Nura Abdullahi, ta bayyana cewa an amince da tallafin ne bayan Gwamnatin Tarayya ta karɓi rahoto kan ɓarnar da ambaliyar ta haifar.
“Gwamnatin Tarayya tana jajanta musu kan yanayin da suka shiga,” in ji ta.
Kayayyakin da aka raba sun haɗa da buhu 500 na shinkafa mai nauyin kilo 25, buhu 500 na masara mai nauyin kilo 25, katan 45 na tumatirin gwangwani, katan 45 na man girki, katan 45 na maggi, da buhu 20 na gishiri.
Sakataren Zartarwa na SEMA, Alhaji Isyaku Kubarachi, ya buƙaci waɗanda suka amfana da su yi amfani da kayayyakin yadda ya dace.
Wani daga cikin waɗanda suka ci gajiyar shirin, Nura Sani, ya nuna jin dadinsa.
“Wannan tallafi zai taimaka mana sosai a wannan mawuyacin lokaci. Muna godiya ga gwamnati bisa ƙoƙarinta,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yansanda Sun Gano Haramtaccen Wurin Hada Makamai A Kano
Rundunar ‘yansandan Nijeriya ta gano wani haramtaccen wurin hada makamai a jihar Kano, lamarin da ya kai ga kama wasu mutane uku tare da kwato bindigogi kirar gida guda 15 tare da harsashi 102. Wadanda ake zargin sun hada da Abdul Sadiq mai shekaru 43; Ahmad Muazu, 22; da Aliyu Sharif, mai shekaru 40, an kama su ne a ranar 10 ga watan Afrilu a unguwar Dorayi Babba da ke jihar, sakamakon wani hadin gwiwa da jami’an rundunar ‘yansandan jihar Kano suka jagoranta. Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna Salah Ya Kafa Tarihi Yayin Da Liverpool Ke Dab Da Lashe Gasar Firimiya Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan, ACP Olumuyiwa Adejobi ya tabbatar da kamen a wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce an gudanar da aikin ne bisa wani sahihan bayanai da suka kai ga gano tarin haramtattun makaman. Sufeto-Janar na ‘yansanda, IGP Kayode Egbetokun, ya yaba da matakin gaggawar da jami’an suka dauka tare da jaddada aniyar rundunar na dakile yaduwar makamai marasa lasisi a fadin kasar nan.Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp