Aminiya:
2025-04-14@19:00:02 GMT

Haɗarin mota ya laƙume rayuka 12 a Neja

Published: 22nd, February 2025 GMT

Aƙalla mutum 12 — ciki har da mata huɗu da maza takwas — sun riga mu gidan gaskiya a sanadiyyar wani mummunan haɗarin mota da ya auku a kan hanyar Lapai zuwa Agaie da ke Jihar Neja.

Wani da lamarin na safiyar wannan Asabar ɗin ya faru a kan idonsa, ya shaida wa Aminiya cewa uku daga cikin matan da suka rasu ’yan gida ɗaya ne.

Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kano ta raba kayan tallafi Ɗan Abacha ya kare mahaifinsa bayan ƙaddamar da littafin IBB

Sai dai wasu fasinjoji uku da suka haɗa da mata biyu da direban motar sun tsallake rijiya da baya, inda a yanzu suke samun kulawa a Babban Asibitin Lapai.

Bayanai sun ce haɗarin ya auku ne bayan wata taho-mu-gama da aka yi tsakanin wata mota ƙirar bas ɗauke da fasinjoji 15 da kuma wata tirela a daidai ƙauyen Nami.

Da yake zantawa da Aminiya ta wayar tarho, direban motar, Mohammed Baba, ya ce lamarin ya auku ne a yayin da suke kan hanyar tafiya Ƙaramar Hukumar Katcha bayan sun taso daga tashar mota ta Kasuwar Gwari da ke birnin Minna.

Direban ya alaƙanta haɗarin da tsautsayi wanda ya ce ya auku ne yayin da direban tirelan ya yi yunƙurin ƙetare wata mota da ke gabansa, lamarin da ya janyo motocin suka yi karo da juna.

Sai dai ya ce tuni direban tirelan ya arce da bayan faruwar lamarin.

Kwamandan Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa FRSC shiyyar Neja, Kumar Tsukwam, ya tabbatar da faruwar lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Haɗarin mota Jihar Neja

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa

Rundunar ‘Yansandan Jihar Adamawa ta kama Umar Shaibu bisa zargin cin zarafin wata mata a yankin Jimeta a jihar. An kama Shaibu ne bayan wani bidiyo mai tayar da hankali ya yadu a kafafen sada zumunta, kamar yadda Jami’in hulda da Jama’a na ‘Yansandan Jihar Adamawa, SP Suleiman Nguroje, ya bayyana. Salamatu Yakubu, matar mai shekaru 22 daga Angwan Tana, an ce wanda ake zargin ya yi ma ta dukan jakin ne mai tsanani, Shaibu, wanda ake cewa shi ne dan uwanta.

Wannan lamarin ya janyo zarge-zargen daga al’umma da kuma kiran da aka yi wa Yansanda daga mutanen gari, da kungiyoyin fararen hula, da sauran masu rajin kare hakkin bil’adama domin a kama wanda ake zargi.

Ƴansanda Sun Kama  Ɓarayin Waya Masu Amfani Da Keke Napep A Adamawa An Kama Wanda Ake Zargi Da Kashe Mai PoS A Adamawa

An kama Shaibu ne tare da taimakon al’umma ta hanyar dabarun kula da tsaro na cikin gari. An tura matar da aka yi wa dukan cutar zuwa asibiti domin samun kulawar likita.

A halin yanzu, wanda ake zargin yana tsare a sashin binciken laifuka na musamman na Jihar (SCID) a sashin kula da mata domin a gudanar da cikakken bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu. Rundunar Yansandan ta tabbatar wa da jama’a cewa za a binciki lamarin sosai kuma wanda ake zargi zai fuskanci shari’a bisa dokokin da suka dace.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa
  • Mutum 45 Sun Rasa Rayukansu A Wani Sabon Hari A Filato 
  • Hatsarin Mota Ya Hallaka Mutum Ɗaya A Bauchi, Wasu Sun Jikkata
  • Ukraine na Fuskantar Wata Barazana, Dangane Da Bukatar Amurka Na Kwace Iko Da Cibiyar Gas Na Rasha  A cikin Kasar
  • Ta kai ƙarar kamfanin jirgi da fasinja kan kukan yaro
  • Shugaban Burkina Faso Ya Yi Fatali Da Tayin Saudiyya Na Gina Masallatai 200 A Kasarsa
  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • Mutane Da Yawa Sun Jikkata Bayan Fashewar Bam A Wata Kasuwa A Ikeja
  • NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi
  • An kashe mutum kan zargin satar kare a Bauchi