Leadership News Hausa:
2025-02-22@22:04:22 GMT

David Moyes Ba Kanwar Lasa Bane A Harkar Ƙwallon Ƙafa – Amorim

Published: 22nd, February 2025 GMT

David Moyes Ba Kanwar Lasa Bane A Harkar Ƙwallon Ƙafa – Amorim

Kocin Manchester United Ruben Amorim ya bayyan cewar Kocin ƙungiyar ƙwallon kafa ta Everton David Moyes ba mutum ne wanda za a raina iyawarshi a harkar kwallon ƙafa ba, David Moyes ya na yin aiki mai kyau na farfado da Everton fiye da yadda na ke yi cikin ƙanƙanin lokaci a Old Trafford inji Amorim.

Amorim zai fafata da Kocin Everton Moyes a ranar Asabar yayin da yake kokarin fitar da United daga koma bayan da ta ke fuskanta, tsohon kocin na Sporting Lisbon ya lashe wasanni huɗu ya yi rashin nasara a wasanni takwas a wasannin gasar Firimiya 12 da ya jagoranci Manche’ster United tun bayan zuwanshi a watan Nuwamba.

Juma Bah: Balladolid Za Ta Kai Manchester City Kara Gaban Kotu Juma Bah: Balladolid Za Ta Kai Manchester City Kara Gaban Kotu

Moyes, wanda United ta sallama a shekarar 2014 bayan ƙasa da shekara guda yana jan ragamar horar da ‘yan wasan, tuni ya samu adadin nasarorin da Amorim ya samu tun bayan zuwanshi Old Trafford duk da cewa wasanni shida kacal ya jagoranta tun bayan komawarsa Everton a watan Janairu.

Everton, a matsayi na 14, tana sama da United wadda ta ke matsayi na 15 a teburin Firimiya gabanin haduwar kungiyoyin na karshe a Goodison Park,Everton wadda akewa lakabi da Toffees za su koma wani sabon filin wasa a kakar wasa mai zuwa.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗan Abacha ya kare mahaifinsa bayan ƙaddamar da littafin IBB

Sadiq S. Abacha, ɗan Tsohon Shugaban Mulkin Soji na Najeriya, Janar Sani Abacha, ya bayyana mahaifinsa s matsayin mutum mai nagarta duk da sukar da ake yi masa har yanzu.

A wani rubutu da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Sadiq, ya ce an jima ana cin amanar mahaifinsa, amma tarihi zai yanke masa hukunci ta hanyar yin adalci.

Sibil Difens ta cafke mutum 17 kan aikata sata a Yobe Dalilan ƙara kuɗin Jami’ar Gombe — Gwamna Inuwa

“Mutumin nan Abacha—kullum sukarsa da cin amanarsa kuke yi a asirce. Tarihi zai tuna ka a matsayin shugaba nagari, ko da kuwa sun ci gaba da ƙoƙarin rage maka ƙima.

“A matsayina na ɗanka, yau na fi alfahari da kai. Lallai kai ne mutumin da suke so sun zama ko da rabinka ne kuwa,” in ji shi.

Ya kammala rubutunsa da karin maganar Hausawa: “Duk wanda ya yi jifa a kasuwa…”

Rubutun nasa ya zo ne kwanaki kaɗan bayan tsohon shugaban mulkin soja, Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya ƙaddamar da littafinsa.

Littafin ya jawo cece-kuce sosai, musamman kan soke zaɓen ranar 12 ga watan Yunin 1993.

A cikin littafin, Babangida ya tabbatar da cewar MKO Abiola ne ya lashe zaɓen, amma ya ce wasu a cikin gwamnatinsa, musamman Abacha, suka tilasta masa soke sakamakon zaɓen.

Janar Sani Abacha ya mulki Najeriya daga 1993 zuwa lokacin rasuwarsa a 1998.

Wasu na yaba wa mulkinsa saboda gyaran tattalin arziƙi da tsaro, yayin da wasu ke sukarsa bisa cin hanci da take hakkin ɗan Adam.

A gefe guda kuma, Gumsu Abacha, ɗaya daga cikin ’ya’yan marigayin, ta mayar martani game da littafin da IBB ya ƙaddamar.

A wani saƙo gajere da ta wallafa a shafin X (Twitter), wanda ke kama da habaici.

Haka kuma, ta sake wallafa wasu rubuce-rubuce da ke cewa Babangida ya zargi Abacha da laifuka ne domin ba shi da ikon kare kansa.

Ga hotunan a ƙasa:

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Har Yanzu Mahaifina Abacha Ne Ya Tsone Musu Ido – Sadiq Abacha
  • Akwai Babban Aiki A Gabana, Cewar Amorim
  • Ɗan Abacha ya kare mahaifinsa bayan ƙaddamar da littafin IBB
  • An Kammala Taron Ƙungiyar AU Na 38 A Ƙasar Habasha
  • Najeriya ta taɓarɓare bayan mulkin IBB – Obi
  • Ba ni da hannu a kisan Dele Giwa — Janar Babangida
  • Abiola Ne Ya Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Na 12 Ga Watan Yuni 1993 – Janar IBB
  • Real Madrid ta fitar da Man City a Gasar Zakarun Turai
  • UCL: Real Madrid ta murƙushe Man City da ci 3