Leadership News Hausa:
2025-04-14@19:16:26 GMT

David Moyes Ba Kanwar Lasa Bane A Harkar Ƙwallon Ƙafa – Amorim

Published: 22nd, February 2025 GMT

David Moyes Ba Kanwar Lasa Bane A Harkar Ƙwallon Ƙafa – Amorim

Kocin Manchester United Ruben Amorim ya bayyan cewar Kocin ƙungiyar ƙwallon kafa ta Everton David Moyes ba mutum ne wanda za a raina iyawarshi a harkar kwallon ƙafa ba, David Moyes ya na yin aiki mai kyau na farfado da Everton fiye da yadda na ke yi cikin ƙanƙanin lokaci a Old Trafford inji Amorim.

Amorim zai fafata da Kocin Everton Moyes a ranar Asabar yayin da yake kokarin fitar da United daga koma bayan da ta ke fuskanta, tsohon kocin na Sporting Lisbon ya lashe wasanni huɗu ya yi rashin nasara a wasanni takwas a wasannin gasar Firimiya 12 da ya jagoranci Manche’ster United tun bayan zuwanshi a watan Nuwamba.

Juma Bah: Balladolid Za Ta Kai Manchester City Kara Gaban Kotu Juma Bah: Balladolid Za Ta Kai Manchester City Kara Gaban Kotu

Moyes, wanda United ta sallama a shekarar 2014 bayan ƙasa da shekara guda yana jan ragamar horar da ‘yan wasan, tuni ya samu adadin nasarorin da Amorim ya samu tun bayan zuwanshi Old Trafford duk da cewa wasanni shida kacal ya jagoranta tun bayan komawarsa Everton a watan Janairu.

Everton, a matsayi na 14, tana sama da United wadda ta ke matsayi na 15 a teburin Firimiya gabanin haduwar kungiyoyin na karshe a Goodison Park,Everton wadda akewa lakabi da Toffees za su koma wani sabon filin wasa a kakar wasa mai zuwa.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da Sifaniya Sun Daga Matsayin Hadin Gwiwa A Fannin Shirya Fina-finai

Wannan gargadi da Sin da EU suka gabatar ga manyan kamfanonin shirya fina-finai da na fasaha na Amurka, na nuna cewa, gangancin da gwamnatin Amurka ke yi na kakaba haraji barkatai, zai ci gaba da illata kashin bayan fannoninta na cinikayya.

 

Hadin gwiwa tsakanin Sin da Sifaniya, ya kara bayyana yadda Sin ke fatan ci gaba da bude kofarta, da aiki tare da abokan hulda irinsu Sifaniya wajen goyon bayan tsarin cudanyar sassa daban daban, da goyon bayan dunkulewar salon raya tattalin arziki da cinikayya marar shinge, da samar da karin hidimomi, da kayayyaki masu inganci ga kasashen biyu ta hanyar hadin gwiwa da juna, da mutunta juna, da amfanar da al’ummunsu. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Turai na E3 sun goyi bayan tattaunawar Iran da Amurka
  • Salah Ya Kafa Tarihi Yayin Da Liverpool Ke Dab Da Lashe Gasar Firimiya
  • Sin Da Sifaniya Sun Daga Matsayin Hadin Gwiwa A Fannin Shirya Fina-finai
  • Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu
  • Newcastle Na Gab Da Samun Gurbi A Gasar Zakarun Turai
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  • Tsohon Kocin Super Eagles, Christian Chukwu, Ya Rasu Yana Da Shekaru 74
  • Abubuwa Da Yawa Na Faruwa Ba Tare Da Sanin Tinubu Ba – Tsohon Ma’aikacin Aso Rock
  • Mahaifi ya yi wa ’yarsa ciki a Bauchi