Ko Real Madrid za ta iya lashe Gasar Zakarun Turai bana?
Published: 22nd, February 2025 GMT
A jiya Juma’a ce aka fitar da jadawalin zagayen ’yan 16 na Gasar Zakarun Turai ta bana a birnin Nyon.
Hukumar Ƙwallon Ƙafar Turai, UEFA, ta tsara yadda zagayen na ‘yan 16 da zagayen dab da na kusa da na ƙarshe da zagayen dab da ƙarshe da kuma zagayen ƙarshe za su kasance.
Haɗarin mota ya laƙume rayuka 12 a Neja Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kano ta raba kayan tallafiZa a kece raini ne a karawar farko ta zagayen ’yan 16 a ranakun 4 da 5 na watan Maris, inda za a yi karon-batta a karawa ta biyu bayan mako guda.
Mai riƙe da kambun gasar Real Madrid za ta kara da abokiyar hamayyarta na birni Atletico Madrid a maimaicin fafatawar ƙarshe na shekarun 2014 da 2016, waɗanda dukkaninsu Los Blancos ce ta samu galaba.
Liverpool za ta kece raini da takwararta Paris Saint-Germain a ɗaya daga cikin fafatawar da za su ɗauki hankali.
Bayern Munich za ta haɗu da abokiyar hamayyarta ta kasar Jamus Bayer Leverkusen, yayin da Arsenal za ta kara da PSV Eindhoven sannan Inter Milan za ta tunkari Feyenoord.
Barcelona za ta barje gumi da Benfica yayin da aston villa za ta hadu da Brugge, ita kuwa Borussia Dortmund za ta hadu da kungiyar Lille ta kasar Faransa.
Madrid wadda ta shiga cikin sahun masu neman gurbin zuwa zagayen ’yan 16 a kakar bana, ta yi waje rod da Manchester City wajen cimma wannan nasara.
Real Madrid ta sake doke Manchester City da ci 3 da 1 a filin wasa na Bernabeu, jimilla 6-2 a karawar da suka yi kashi biyu — gida da waje.
Madrid ta ce karɓi baƙuncin Manchester City a wasan karawa ta biyu bayan doke ta a gida (Etihad) da ci 3 da 2.
Ko a bara dai Real Madrid ce ta lashe gasar karo na 15 kuma mafi bajinta la’akari da cewa mataki ne da ba a taɓa samun wata ƙungiya ta yi makamancinsa ba a tarihi.
A karawar ƙarshe da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Borussia Dortmundta Jamus a filin wasa na Wembley, Real Madrid ta lallasa Jamusawan da ci 2-0.
Godiya ga ɗan wasan bayan Real Madrid, Dani Carvajal wanda shi ne ya yi kukan kura ya fara zura wa Dortmund ƙwallon farko a mintuna na 74 yayin da ɗan wasa Vinicius Junior shi ma ya gwada sa’arsa ya zura wa ƙungiyar ƙwallon ƙafar Jamus ɗin ƙwallo ta biyu a yayin da ake mintuna 83 da fara wasan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gasar Zakarun Turai
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Hamas Zata Saki Fursunoni 6, Yayin Da’Yan Sahayoniyya Zasu Saki Fursunonin Falasdinawa 602
Dakarun Izzuddeen Al-Qassam bangaren sojin kungiyar Hamas zai saki fursunonin ‘yan sahayoniyya guda 6 a madadin fursunonin Falasɗinawa 602
A cikin tsarin yarjejeniyar musayar fursunoni na Ambaliyar Al-Aqsa da kuma a cikin kashi na bakwai na matakin farko na shirin musaya … za a sako wasu sabbin fursunonin Isra’ila guda 6 da suke hannun dakarun Al-Qassam bangaren sojin kungiyar Hamas, a ranar Asabar, tare da bayyana sunayensu.
A sakamakon haka, mamayar za ta saki fursunonin Falasdinawa 602: Falasdinawa 50 daga cikinsu an yanke musu hukuncin daurin rai da rai ne, wasu 60 daga cikinsu kuma an yanke musu hukunci mai tsawo, da kuma fursunoni 47 na Wafa al-Ahrar da aka sake kama su, bayan zaman gidan yari a baya. Haka nan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila zata saki fursunonin Falasdinawa 445daga cikinmazauna Gaza wadanda aka kama su bayan ranar 7 ga watan Oktoban shekara ta 2023.
Fursunonin Isra’ila shida da za a sako a ranar Asabar din nan, za a kara da fursunoni goma sha tara masu rai da kuma matattun yahudawan sahayoniyya guda hudu da gwamnatin Isra’ila ta karbe su tun bayan da aka cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza da ta fara aiki kwanaki 34 da suka gabata.