Yake-Yaken Kasa Da Kasa Ne Suka Mamaye Taron G20 Na Ministocin Harkokin Wajen Kungiyar A Afirka Ta Kudu
Published: 22nd, February 2025 GMT
A jiya Jumma’a ce aka kammala taron kungiyar kasashen G20 a birnin johanasboug na kasar Afrika ta Kudu, kuma inda batun yake-yake a yankunan daban-daban na duniya ne suka mamaye taron.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa yakin Ukraine da Rasha Hamas da HKI, Congo da sauransu ne suka mamaye taron inda ministocin harkokin wajen kasashen na G20 suka tattauna a kansu.
Ministan harkokin wajen na kasar Afrika ta Kudu Ronal Ramola ya bayyana cewa duk tare da cewa babu wani babban jami’an gwamnatin kasar Amurka a taron amma taron ya gudana kamar yadda ake saba.
Kungiyar G20 Taron kasashe masu arziki a duniya, wadanda suke da kasha 85% na tattalin arziki a duniya sannan suna da kasha 3/4 na harkokin kasuwanci a duniya.
Wannan ne karon farko wanda aka gudanar da taron a nahiyar afrrika, kuma a cikin watan Nuwamba na wannan shekaran ne za’a gudanar da taron shuwagabannin kasashen sannan Amurka ce zata karbi shugabancin kungiyar daga hannun afirka ta kudu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar
Iran, ta yi Allah wadai da harin ta’addancin da ya yi sanadin mutuwar gomman mutane a wani masallaci a kudu maso yammacin Jamhuriyar Nijar.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmaeil Baghaei ya yi kakkausar suka kan harin da aka kai wa masallata.
Akalla mutane 44 ne suka mutu yayin da 13 suka jikkata a harin da aka kai a kauyen Fonbita da ke cikin kauyan Kokorou dake jihar Tillabery wanda ya faru a lokacin da wasu ‘yan ta’addan na kungiyar Da’ish a yankin Sahara (ISGS) suka far wa masallacin, inda suka auka wa masu ibada dake sallar Juma’a.
Baghaei ya bayyana cewa, wannan ta’addancin da aka aikata a lokacin sallar Juma’a ya saba wa ka’idar Musulunci, kuma ya saba wa dukkanin ka’idojin shari’a da hakkin dan Adam na kasa da kasa.
Kakakin na Iran ya jaddada muhimmancin kara inganta hadin gwiwa a matakai daban-daban na shiyya-shiyya da na kasa da kasa don dakile da yaki da ta’addanci.
Ya zama dole a gurfanar da masu hannu a harin ta’addanci da kuma hukunta su.
Baghaei ya nuna juyayi ga iyalan wadanda harin ya rutsa da su da gwamnati da kuma al’ummar Nijar kan harin ta’addanci.