Sojojin kasa na jumhuriyar Musulunci ta Iran sun hada guiwa da sojojin ruwa don atisayen hadin guiwa wanda suka sanyawa suna Zulfikar 1403.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakain atisayen Brigadier General Alireza Sheikh yqana cewa a cikin wannan atisayen suna son gwada aiki tare da sojojin masu aiki a sama da na ruwa don samar da yanayi irin na yanayi yaki da gaske don fahintar da harkokin yaki suke tafiya.

General Alireza Sheikh yace a bangare na farko na wannan atisayen mun gwada yadda jiragen yakin masu saukar ungulu zasu sauka su tashi a dai dai lokacinda ake cikin budewa juna wuta da makiya.

Sannan manufar atisayen gaba daya itace samar da yanayi ta yadda bangarorin sojojin kasar zasu yi aiki tare a lokacin yaki, ko wane bangare yana aiki a bangaren da ya kore a kai amma kuma suna yakar makiyi guda.

Ya ce zasu yi amfani da jiragen yaki masu saukar ungulu, jiragen yaki na sojoji, masu saukar ungulu nau’in Cobra RH, SH da kuma AB212.. Sannan ana wannan atisayen ne a tashar jiragen ruwa na sojojin kasar dake Makron. Gabaki dayan atisayen na karkashin shi’arin Zulfikar 1403 ne.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Masu Sana’ar Kamun Kifi Sun Koka Kan Ƙarancin Kuɗaɗen Shiga A Taraba

daya daga cikin masu sana’ar a yankin Yashin Tuwo a karamar Hukumar Karim-Lamido a jihar, Mallam Dauda Adamu, ya tabbatar da wannan kalubalen da masu sana’ar ke fuskanta a jihar, inda ya sanar da cewa, lamarin ya tilasta wasu masu sana’ar rungumar aikin noma da kama wasu sana’oin daban, domin samun kudaden shiga.

“A baya masu sana’ar a kullum suna samun kudaden shiga masu yawan gaske, sai dai; saboda raguwar Kifin a Koguna, kudaden shigar da suke samu sun ragu”, in ji Dauda.

Wani jami’i a Ma’aikatar Aikin Gona ta Jihar, wanda bai bukaci a ambaci sunansa ba, ya tabbatar da wannan raguwa ta Kifin a Kogunan jihar.

Kazalika, Mallam Dauda ya alakanta wannan kalubalen kan irin yanayin kamun Kifin da masu sana’ar ke yi, samun sauyin yanayi da kuma yin amfani da wasu sinadaran kamun Kifin da masu sana’ar ke yi a jihar, wadanda ya ce, su ne manyan ummul haba’isin matsalar da ta shafi fannin.

Ya bayyana cewa, za a iya magance wannan matsalar, a kwanakin baya; Ma’ikatar Aikin Gona ta jihar, ta kaddamar da gangamin ilimantar da kan masu sana’ar kamun Kifin a jihar, musamman kan kamun Kifin ba bisa ka’ida ba.

Kazalika, Mallam Dauda ya ce; ma’aikatar ta kuma raba wa masu sana’ar kamun Kifin ingantattun Rigar kamun Kifin da kuma sauran kayan aikin kamunsa, domin daina yin kamun Kifin ba bisa ka’ida ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Luguden Wuta Kan Gabar Yammacin Kogin Jordan
  • Sojojin Faransa Sun Mika Sansanin Soji Mafi Girma Da Suka Mamaye Ga Sojojin Faransa
  • Masu Sana’ar Kamun Kifi Sun Koka Kan Ƙarancin Kuɗaɗen Shiga A Taraba
  • Tashar Jiragen Sama Ta Rafikul Hariri Int. Na Birnin Beirut Yana Ciki Da Masu Shiga Kasar Saboda Jana’izar Shaheed Nasarallah
  • Babu Wani Abin Burgewa A APC, Za Mu Kori Wannan Gwamnati A 2027 – Tambuwal
  • An haramta wa manyan tireloli aiki a Najeriya
  • Dubban Falasdinawa Sun Kauracewa Gidajensu A Dai-Dai Lokacinta Sojojin HKI Suke Fafatawa Da Dakarun Falasdinawa
  • Gwamnati Za Ta Haramta Amfani Da Tankoki Masu Ɗaukar Lita 60,000 Aiki Daga Maris 1
  • IRGC Ta Kaddamar Da Sabbin Makamai A Atisayen Da Take Yi A Halin Yanzu