Leadership News Hausa:
2025-02-23@05:10:49 GMT

Mataimakin Firaministan Sin Ya Zanta Da Sakataren Baitulmalin Amurka

Published: 22nd, February 2025 GMT

Mataimakin Firaministan Sin Ya Zanta Da Sakataren Baitulmalin Amurka

Jagoran kula da harkokin tattalin arziki da kasuwanci na kasashen Sin da Amurka a bangaren Sin, wanda kuma shi ne mataimakin firaministan kasar Sin, He Lifeng, ya zanta da sakataren baitulmalin Amurka, Scott Bessent, ta kafar bidiyo jiya Jumma’a 21 ga wata, inda suka yi musanyar ra’ayoyi kan wasu muhimman batutuwan da suka shafi tattalin arzikin kasashen biyu, bisa matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma.

Bangarorin biyu duk sun amince da muhimmancin alakokin tattalin arziki da kasuwanci a tsakaninsu, inda suka yarda su ci gaba da tuntubar juna kan batutuwan da suka fi daukar hankulansu.

Har wa yau, kasar Sin ta nuna matukar damuwa kan matakin da Amurka ta dauka kwanan nan, na kara sanya wa hajojin kasar Sin harajin kwastam. (Murtala Zhang)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Trump Yana Son Ganin Bayan Shugaban Kasar Ukraine Volodimir Zelezky Daga Kujerar Shugabancin Kasarsa

A dai-dai lokacinda shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bayyana a fili kan cewa baya son nganin tokwaransa na kasar Ukraine Volodimir Zelesky kan kujerar shugabancin kasarsa. Al-amura suna kara tabarbarewa a Kiev.

Jaridar Economist ta kasar Burtaniya ta bayyana cewa al-amarin ya bayyana kiri-kiri ne a lokacinda shugaban kasar Amurka ya zanta ta wayar tarho da shugaban kasar Rasha Vladimi Putin. Sannan aka gudanar da taro na farko tsakanin Amurka da Rasha a birnin riyad na kasar Saudiya ba tare da an gayyaci Zelesky ba haka ma, babu wani Jami’in tarayyar Turai da aka gayyata.

Jaridar ta nakalto wani babban jami’in gwamnati a Kiev yana cewa tun lokacinda suka fahinci cewa Trump baya son a ci gaba da yaki a Ukraine, sannan baya son shugaba Zeleski sun san haka zai faru.

Banda haka, Trump ya bayyana cewa Amurka ta kashe dalar Amurka miliyon 360 kan yakin da ta tabbatar da cewa Ukrain ba zata sami nasara ba. Banda wannan ya ji ta bakin Zeleski kansa kan cewa an sace rabin kudaden da Amurka ta bata.  A halin yanzu dai Trump ya bukaci a gudanar da zabe a kasar Ukraine, don ya tabbatar da cewa Zelesky bai da magoya baya da yawa. A cikin watan Fabrairun da mukr ciki ne yaki tsakanin Ukraine da Rasha yake cika shekaru 3 da fara shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yake-Yaken Kasa Da Kasa Ne Suka Mamaye Taron G20 Na Ministocin Harkokin Wajen Kungiyar A Afirka Ta Kudu
  • Sojojin Faransa Sun Mika Sansanin Soji Mafi Girma Da Suka Mamaye Ga Sojojin Faransa
  • Turji Ya Ƙaƙaba Wa Ƙauyen Mataimakin Gwamnan Sokoto Da Wasu Biyan Harajin Miliyan 22
  • Ɗanyen Mai Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Ƙaru A Watan Janairun 2025 –OPEC
  • Amurka Ta Bawa HKI Makami Mai Karfi, MK-87
  • MDD Ta CE Sake Tada Komatsar Tattalin Arzikin Kasar Siriya Zau Dauki Shekaru 50 Nan Gaba
  • Trump Yana Son Ganin Bayan Shugaban Kasar Ukraine Volodimir Zelezky Daga Kujerar Shugabancin Kasarsa
  • Jakadan Sin Dake Najeriya Ya Gana Da Karamar Ministar Harkokin Wajen Kasar
  •  Jagora: Siyasar Kasar  Iran  Ta Ginu Ne Akan Kyautata Alaka Da Kasashen Makwabta