Aminiya:
2025-02-23@04:43:26 GMT

An haifi alade mai fuskar mutum a Philippines

Published: 22nd, February 2025 GMT

Mamallakin aladiyar da ta haihu mai suna Alfredo Cardinas Junior, ya firgita bayan da ɗaya daga cikin aladun nasa ta haihu yana kallo, inda ya ji sautin kukan ɗan aladen kamar na dan-adam kuma yake kama da na jaririn ɗan-adam.

Jaririn aladen mai siffar mutum yana daga cikin jarirai takwas da aladiyar Mista Cardinas ta haifa kuma babu wani daga cikinsu da aka rawaito cewa ya samu naƙasu.

Haɗarin mota ya laƙume rayuka 12 a Neja Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kano ta raba kayan tallafi

Mai aladen, Alfredo Cardinas Jr, ya bayyana cewa ya firgita sosai a lokacin da aka haifar masa jaririn aladen mai fuskar mutum.

Ya bayyana cewa: “Na ji tsoro sa’ad da na fara ganin jaririn. Na kara gigicewa da na ji kukansa. Na ji kamar irin na jaririn dan-adam.”

An haifi jaririn aladen ne a gidan Alfredo a birnin Tanjay da ke kudu da Manila a kasar Philippines.

Bidiyon jaririn aladen yana kukan da ba a saba ji ba, ya janyo ra’ayoyin jama’a sama da miliyan 1.5 a shafin Fesbuk.

Bidiyon ya nuna aladen da fuska irin ta mutum, amma babu idanu.

Alfredo ya ce, ya dora jaririn aladen a kan bargo a kasa yayin da yake yunkurin motsa jikinsa.

Sannan aka dora shi a kan wani tsohon buhu yayin da yake faman numfashi.

Sai dai bai yi tsawon kwana ba, inda ya mutu sa’o’i hudu kacal da haihuwarsa.

Likitan dabbobi na yankin, Dokta Ma Christine Hope Dejadena, ta ce, ba kasafai ake samun alade daya tak da wata nakasa bayan haihuwa ba.

Sai dai ta yi hasashen cewa, mahaifiyar aladen ta yi ciki da wani nau’in halitta ta daban.

Ta ce: “Aladen ba za ta samu juna biyu daga wani nau’in halitta ta daban ba.”

Madadin haka, ana da tabbacin cewa, an haifi aladen da larurar haihuwa da ake kira ‘holoprosencephaly’, da take haifar da cutar kwakwalwa.

Likitan dabbobi Dakta Aris Miclat ya yi bayanin: “Wannan cuta ce ta haihuwa, wadda a zahiri nakasu ce ta haihuwa.

Jaririn na da cuta da take da alaka da kai da gangar jiki (cephalic), wanda gaban kwakwalwa yake kasa girma zuwa mataki biyu na (cephalic).”

Dokta Miclat ya yi imanin cewa, zai iya kasancewa, mahaifiyar ta harbu da sinadarai ko magungunan kashe kwari yayin da take da ciki, wanda zai iya shafi girman alade a cikin mahaifa.

Ya ce: “Kusan koyaushe, wannan larura ta musamman tana iya sanadiyyar mutuwa.”

Likitan ya kuma musa zargin cewa akwai yuwuwar cudanya tsakanin uwar aladen da dan-adam.

Alfredo ya ce, ba shi ne karon farko da wata daga cikin aladunsa ta haifi alade mai nakasa ba.

A baya yana da alade da aka haifa kamar yana da fuka-fukai, suna fitowa daga jikinsa.

Alfredo ya yi imanin cewa, dabbar ta kawo sa’a ga iyalinsa, saboda ya sami damar saka hannun jari a cikin harkar kiwon shanu da wayar salula jim kadan bayan haihuwarta.

Wani bincike ya gano kusan kashi uku cikin dari na aladu ana haifar su da larura ta haihuwa.

Akalla akan samu alade daya da larura a kusan kashi 17 na cikin dabbobin da ake haihuwa.

Yawancin wadanda ke da nakasar haihuwa sun mutu a cikin mako guda da haihuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fuskar Mutum jaririn aladen

এছাড়াও পড়ুন:

Sibil Difens ta cafke mutum 17 kan aikata sata a Yobe

Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Sibil Difens (NSCDC), a Jihar Yobe, ta kama wasu mutum 17 da ake zargi da satar kayayyakin lantarki, na’urorin sadarwa a jihar.

Kwamandan rundunar, AS Dandaura, ya tabbatar da kamen a Damaturu, Babban Birnin jihar, inda ya ce an gano wuraren ajiya uku da ake amfani da su don ɓoye kayan sata.

Dalilan ƙara kuɗin Jami’ar Gombe — Gwamna Inuwa Gwamnatin Filato ta dakatar da haƙar ma’adinai saboda matsalar tsaro

Ya bayyana cewa samamen da aka kai ya taimaka wajen gano wuraren ajiya guda uku—ɗaya a kusa da ofishin Hukumar Alhazai a Damaturu, na biyu a Duriya bayan sabuwar kasuwa, sai kuma na uku a Abbari bypass.

Dandaura ya ce an kama shugaban wata ƙungiyar dillalan kayayyakin bola a yankin, Aliyu Ajakuta, wanda ake zargi da jagorantar aikata satar.

Haka kuma, an cafke wasu da ake zargi da hannu a laifin, ciki har da Umar Sai’adu mai shekara 17, Mohammed Salisu mai shekara 25.

Sauran sun haɗa da Ali Adam mai shekara 18, Ibrahim Mohammed mai shekara 19, Mohammed Musa mai shekara 20, Abdulhamid Mohammed mai shekara 15 da Hassan Dauda mai shekara 18.

Sauran da aka kama sun haɗa da Alhassan Yakubu mai shekara 26, Mohammed Babagana mai shekara 29, Mohammed Bashiru mai shekara 18, Mohammed Bello mai shekara 17, Adamu Abdullahi Usman mai shekara 20, Mustapha Babagana mai shekara 23, Tijani Bako mai shekara 19, Bashiru Adam mai shekara 18 da Lawal Salisu mai shekara 19.

Hukumar ta bayyana cewa ta ƙwato kayayyaki masu yawa daga hannunsu, ciki har da na’urorin sadarwa, igiyoyi masu sulke, manyan karafunan titin, farantin sola, batura, da sauran kayayyaki.

Kwamandan ya jaddada cewa za a gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban kotu bayan kammala bincike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shan Maganin Fitar Da Zaƙi Kafin Haihuwa
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Alhassan (a) 20
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Alhassan (a) 19
  • Sibil Difens ta cafke mutum 17 kan aikata sata a Yobe
  • Da Ɗumi-ɗumi: Sanata Lawal Yahaya Gumau Ya Rasu Yana Da Shekara 57
  • Thomas Friedman: Trump Yana Son Ci Gaba Da Zama Shugaban Kasar Amurka Har Abada
  • Iran Ta Yi Tir Da Shugaban Hukumar IAEA Saboda Sanya Siyasa Da Daukan Bangare A Jawansa Na Baya Bayan Nan
  • Tashar Jiragen Sama Ta Rafikul Hariri Int. Na Birnin Beirut Yana Ciki Da Masu Shiga Kasar Saboda Jana’izar Shaheed Nasarallah
  • Trump Yana Son Ganin Bayan Shugaban Kasar Ukraine Volodimir Zelezky Daga Kujerar Shugabancin Kasarsa