Leadership News Hausa:
2025-04-14@19:39:12 GMT

Shan Maganin Fitar Da Zaƙi Kafin Haihuwa

Published: 23rd, February 2025 GMT

Shan Maganin Fitar Da Zaƙi Kafin Haihuwa

Sannan dadin abin aka fada amma mene ne illar da ka iya biyo bayansa? Shin hakan ma batun yake a ilmance ko kuwa?

Wannan ta sa da zarar haihuwa ta gabatowa mace kowa sai ka ga shawara yake ba ta akan komai ma, musamman ma atsakaninsu mata, Eh munsan kuna yi ne bisa kyakkyawar manufa da son ku ga ta haihu lafiya, amma fa ba duk ‘yan’adam bane zubin halittarsu tare da komai yai daidai da na juna ba.

Ba mamaki wata kuka ji ta yi irin haka ta wanye lafiya, amma mu tuna fa idan wani ya yi abu ya kwana lafiya to fa wani in ya yi wahala zai sha.

Babu wani abu da sunan zaki jikin mai juna biyu, in aka ce zaki a jika to fa mu ko yaushe a likitance abin da muka sani; ana batu ne na ciwon suga ajikin mutum, wato yawaitar sinadarin Bulkodi a cikin jini.

Shi ko ciwon suga yayin goyon ciki, kuma muddin aka gano shi ba’a wata-wata ake dora mace kan shawarwarin abinci ko magunguna wasu lokutan allura domin ba ta kariya daga hatsarin suga da ka iya tasowa, wanda cikin irin wannan hatsarin akwai mutuwar jariri a ciki, mutuwar macen wajen haihuwa, zubewar ciki, ko sanya jariri ya yi girma fiye da kima a ciki ta yadda ba zai iya fitowa ba sai dai ai aiki a ciro shi, ko kuwa sai an kara fadin wajen kafin kan jariri ya iya wucewa.

Wasu kan dauki kowanne katoton jariri lafiya ce tasa, amma ina wani girman ba na ka’ida bane larura ce, galibi alama ce ta larurar suga yayin goyon ciki a uwar musamman a macen da ba ta rika zuwa awo ba, ko kuwa ba ta samu duk gwaje-gwajen da suka dace ba, kurum an auna arziki ne. Duk jaririn da nauyinsa ya wuce kilogiram 3.5 lafiyar mahaifiyarsa abin tuntuba ce a yayin goyon cikinsa.

Shi kuwa wannan sugan ajini yake ba zai taba fita ta ta gaban mace ba ko ta hanyar fitar da wani ruwa ba.

Za Mu Ci Gaba A Mako Mai Zuwa Idan Allah Ya Kai Mu

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Haihuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Turai na E3 sun goyi bayan tattaunawar Iran da Amurka

Kasashen turan nan guda uku da ake wa lakabi da E3, sun nuna goyon bayansu ga tattaunawar da ake tsakanin Iran da Amurka.

Ministan Birtaniya mai kula da yammacin Asiya Hamish Falconer ne ya bayyana hakan inda ya ce Birtaniya tare da Faransa da Jamus na goyon bayan sasanta batun nukiliyar Iran ta hanyar diflomasiyya.

A cikin sakon da ya wallafa, Falconer ya yaba da tattaunawar da akayi a babban birnin kasar Oman na Muscat a matsayin “muhimmiyar mataki na farko.”

Kuma a cewarsa “Birtaniya, tare da kawayenta na E3, a shirye suke don tallafawa tattaunawar.

A cikin 2018 a lokacin mulkinsa na farko, Trump ya janye Amurka daga yarjejeniyar da aka cimma a baya kan shirin nukiliyar Iran da kuma lafta mata tsauraren takunkumai amma kuma ya nuna aniyar kulla sabuwar yarjejeniya don maye gurbin waccen ta 2015.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Turai na E3 sun goyi bayan tattaunawar Iran da Amurka
  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
  • Janar Tsiga, Mahaifiyar Rarara da muhimman mutane da aka sace a Katsina
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi
  • Iyaye Mata Sun Bukaci A Rika Samar Da Kayayyakin Bada Tazarar Haihuwa Akan Lokaci
  • Mutane Da Yawa Sun Jikkata Bayan Fashewar Bam A Wata Kasuwa A Ikeja
  • NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi
  • Mahaifi ya yi wa ’yarsa ciki a Bauchi