HausaTv:
2025-02-23@11:34:21 GMT

Sojojin Sudan Sun Tsananta Kai Hare-Hare Kan ‘Ya Tawayen Rapid Support Forces

Published: 23rd, February 2025 GMT

Sojojin Sudan na ci gaba da gudanar da ayyukansu na kai farmakin karshe da nufin murkushe ‘yan tawayen Dakarun Kai Daukin Gaggawa

Sojojin Sudan sun fara aikin wanzar da tsaro a wasu yankuna a jihar Al-jazira da ke tsakiyar kasar Sudan, tare da kara tsaurara matakan killace fadar shugaban kasar da ke karkashin ikon dakarun kungiyar Rapid Support Forces, wadanda a halin yanzu mayakan ‘yan tawayen suke fama da karancin kayayyakin aiki.

Sojojin Sudan sun kai farmaki kan dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces da ke kusa da gadar Soba, wadda ta hada kudancin Khartoum da gabashin Nilu a kan hanyar kogin Blue Nile, inda suka kwace iko da sansanonin dakarun ‘yan tawayen. A yayin da Dakarun kai daukin gaggawa suka yi ruwan bama-bamai a yankuna da dama na Gabashin Nile da Umm Dom a birnin Khartoum, inda suka kashe fararen hula 7 tare da jikkata wasu da dama.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Faransa Sun Mika Sansanin Soji Mafi Girma Da Suka Mamaye Ga Sojojin Faransa

Bayan shekaru 47, Faransa ta janye daga sansanin sojinta mafi girma a kasar Ivory Coast

A hukumance Faransa ta mayarwa kasar Ivory Coast babban sansanin soji da ta mamaye kusan shekaru hamsin a kusa da birnin Abidjan, a wani bangare na yarjejeniyar da kasashen biyu suka kulla.

Filin tashar jiragen ruwa na Port Bouet, wanda ke dauke da bataliyar sojoji na 43 da na ruwa, ya shaida bikin mika ta, inda aka daga tutar Ivory Coast a farfajiyar sansanin, kuma an canza sunan ta da sunan babban hafsan soji na farko a Ivory Coast, Thomas Dakine Ouattara, wanda hakan ya kawo karshen kasancewar Faransa a kasar tun shekarar 1978.

Ministan tsaron kasar Ivory Coast, Tene Berahima Ouattara, ya jaddada cewa: Wannan mataki na wakiltar wani sabon mataki na dangantakar abokantaka da hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tsakanin kasashen biyu. A nasa bangaren, ministan tsaron kasar Faransa Sébastien Lecornu ya bayyana cewa: “Duniya tana canjawa, kuma a fili yake cewa dole ne dangantakar kasashen biyu ta bunkasa,” yana mai nuna alfaharinsa ga “dangantakar da aka gina bisa abota da kwarewa tsakanin Faransa da Ivory Coast.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Bukaci Hanzarta Hukunta Shugabannin ‘Yan Sahayoniyya Kan Laifukan Da Suka Aikata
  • Sojojin Ruwa Da Kuma Sojijin Sama Na JMI Sun Hada Guiwa Don Yin atisaye Tare Mai taken Zulfikar
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Sun Jaddada Cewa: Zasu Kai Harin Daukan Fansa Na Alkawarin Gaskiya Kan Isra’ila
  • Sojojin Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Luguden Wuta Kan Gabar Yammacin Kogin Jordan
  • Sojojin Faransa Sun Mika Sansanin Soji Mafi Girma Da Suka Mamaye Ga Sojojin Faransa
  • DRC : Kwamitin Tsaro Na MDD, Ya Yi Da Goyan Bayan Da Rwanda Ke Bai Wa ‘Yan Tawayen M23
  • Babban Kwamandan IRGC Ya Bayyana Cewa: Amurka Da Isra’ila Ba Su Yi Nasara A Yakin Gaza Ba
  • Dakarun Kai Daukin Gaggawa Sun Kashe Mutane Fiye Da 400 A Yankin Al-Qatana Da Ke Jihar White Nile Ta Sudan
  • Shugaba Tinubu Ya Yaba Da Gudunmawar Da IBB Ya Bayar Yayin Mulkinsa