Aminiya:
2025-04-15@23:22:21 GMT

Ɗan shekara 43 ya auri mai shekara 88

Published: 23rd, February 2025 GMT

Ma’aurata da ke da tazarar shekaru 45 sun shawo kan masu zolayarsu da batun kiwon lafiya don samun farin ciki na musamman a baya kuma sun ce sun ki jin kunyar waɗansu ba su fahimci alakar aurensu ba.

Ma’auratan sun shawo kan matsalar da za ta iya shafan huldarsu da wadanda ke son raba aurensu – amma duk da haka sun nace za su yi iya kokarinsu don hana su farin ciki a rayuwar auren.

PDP ta lashe zaɓen ƙananan hukumomin Osun Wani mutum ya yi wa agolarsa fyaɗe ta samu juna biyu

Adrián Narbáez, mai shekara 43 yanzu ya hadu da matarsa Delia Lúkuez mai shekara 88, a wani baje kolin fasaha a shekara ta 1998, tun yana dan shekara 16, ita kuma tana da shekara 61.

Da farko, ma’auratan abokai ne kawai, saboda sun hada kai a kan abubuwan da suke so kan kirkirar fasaha.

Malama Delia ta kasance kwararriya mai sha’awar fentin, yayin da Adrián yake son rubutun wakoki da tatsuniyoyi.

Bayan haduwarsu ta farko, Adrián da Delia sun ci gaba da tuntubar juna, suna musayar wasiku, wanda Adrián yake yi har yau.

Yayin da shekaru suka shige, abokantakarsu ta zama soyayya, kuma Adrián, wanda yake jin kamar an haife shi a lokacin da bai dace ba, ya fada wa Delia cewa yana son ta.

Dangantakarsu ta yi danko, amma tsawon wata 12, sun zabi su boye soyayyarsu—suna haduwa lokaci zuwa lokaci.

Ma’auratan, wadanda suke zaune a garin Ribadabia, Mendoza da ke Argentina, sun bi ka’idojin addininsu kuma ba su iya kadaita da juna a wani wuri ba.

Haka kuma sun ta cin karo da kalubale da zarar sun yanke shawarar fitowa fili da soyayyarsu.

Kamar yadda Delia ta bayyana wa manema labarai na gida, ba kowa ne ke farin ciki game da dangantakarsu ba.

Ta bayyana cewa: “Mahaifin mijina ya karbe ni nan da nan, amma mahaifiyarsa ba ta so.”

Adrián, wanda ya ce ya fi son tsofaffin samfuran mota da gidaje, ya kara da cewa: “Zolaya ce, ba su fahimci cewa, duk da bambancin shekaru, za mu iya son junanmu. Da farko, sun yi duk mai yiwuwa domin su raba mu.”

Amma duk da manyan matsalolin da suka fuskanta, kaunar junansu ta yi nasara a karshe.

Adrián, wanda kodayake matashi ne, bai taba sha’awar mata masu irin shekarunsa ba, inda ya bayyana wa kafar yada labarai ta Infobae cewa: “Ban taba jin kunyar bambancin shekarun ba.

“A gaskiya, ban lura da shi ba. Kuma kodayake akwai shekaru 45 a tsakaninmu, ina tafiya tare da ita ko’ina.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Adrián Narbáez

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan

Hukumar kula da agaji ta MDD (OCHA) ta bada sanarwan cewa, gwamnatin HKI a yankin yamma da kogin Jordan ta kori Falasdinawa a gidaje 5 a yankin bayan sun rusa gidajensu. Hukumar ta kara da cewa wadanda HKI ta rusa gidajensu a yankin sun hada da yara 19 da da iyayensu 33 maza da mata 6.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto OCHA na cewa tun watan Maris da ya gabata zuwa yanzu, HKI ta rusa gidaje da gine-ginen Fafalsadinawa kimani 100 a yankin yamma da kogin Jordan wadanda suka hada da gabacin birnin Qudus da kuma sauran yankuna, da sunan an gina gidajen ba bisa ka’ida ba.

Banda haka suna kwace gonakin Falasdinawa don ginawa sabin yahudawan da suke shigowa kasar matsugunai.

Labarin y ace, a wasu lokutan yahudawan zasu tilastawa Falasdinawa rusa gidajensu da kansu ko kuma idan sun rusa su da kayan aikinsu su tilastawa Falasdinawan kbiyan kudaden aikin rusawan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yanke Masa Hukuncin Ɗaurin shekaru 2 A Gidan Yari Saboda Yunƙurin Daɓa Wa Mahaifinsa Almakashi A Kano
  • Matashi ya yi yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a Kano
  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa
  • ’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta
  • Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran
  • Sojojin Yemen Sun Kakkabo Jirgin Yakin Amurka Wanda Ake Sarrafa Shi Daga Nesa Na 19
  • Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan
  • Firaministan Kasar Laos: Kasar Sin Abar Koyi Ce a Fannin Kawar Da Talauci
  • Mutum ɗaya ya mutu a faɗan ƙungiyar asiri a Maiduguri
  • Janar Tsiga, Mahaifiyar Rarara da muhimman mutane da aka sace a Katsina