Ɗan shekara 43 ya auri mai shekara 88
Published: 23rd, February 2025 GMT
Ma’aurata da ke da tazarar shekaru 45 sun shawo kan masu zolayarsu da batun kiwon lafiya don samun farin ciki na musamman a baya kuma sun ce sun ki jin kunyar waɗansu ba su fahimci alakar aurensu ba.
Ma’auratan sun shawo kan matsalar da za ta iya shafan huldarsu da wadanda ke son raba aurensu – amma duk da haka sun nace za su yi iya kokarinsu don hana su farin ciki a rayuwar auren.
Adrián Narbáez, mai shekara 43 yanzu ya hadu da matarsa Delia Lúkuez mai shekara 88, a wani baje kolin fasaha a shekara ta 1998, tun yana dan shekara 16, ita kuma tana da shekara 61.
Da farko, ma’auratan abokai ne kawai, saboda sun hada kai a kan abubuwan da suke so kan kirkirar fasaha.
Malama Delia ta kasance kwararriya mai sha’awar fentin, yayin da Adrián yake son rubutun wakoki da tatsuniyoyi.
Bayan haduwarsu ta farko, Adrián da Delia sun ci gaba da tuntubar juna, suna musayar wasiku, wanda Adrián yake yi har yau.
Yayin da shekaru suka shige, abokantakarsu ta zama soyayya, kuma Adrián, wanda yake jin kamar an haife shi a lokacin da bai dace ba, ya fada wa Delia cewa yana son ta.
Dangantakarsu ta yi danko, amma tsawon wata 12, sun zabi su boye soyayyarsu—suna haduwa lokaci zuwa lokaci.
Ma’auratan, wadanda suke zaune a garin Ribadabia, Mendoza da ke Argentina, sun bi ka’idojin addininsu kuma ba su iya kadaita da juna a wani wuri ba.
Haka kuma sun ta cin karo da kalubale da zarar sun yanke shawarar fitowa fili da soyayyarsu.
Kamar yadda Delia ta bayyana wa manema labarai na gida, ba kowa ne ke farin ciki game da dangantakarsu ba.
Ta bayyana cewa: “Mahaifin mijina ya karbe ni nan da nan, amma mahaifiyarsa ba ta so.”
Adrián, wanda ya ce ya fi son tsofaffin samfuran mota da gidaje, ya kara da cewa: “Zolaya ce, ba su fahimci cewa, duk da bambancin shekaru, za mu iya son junanmu. Da farko, sun yi duk mai yiwuwa domin su raba mu.”
Amma duk da manyan matsalolin da suka fuskanta, kaunar junansu ta yi nasara a karshe.
Adrián, wanda kodayake matashi ne, bai taba sha’awar mata masu irin shekarunsa ba, inda ya bayyana wa kafar yada labarai ta Infobae cewa: “Ban taba jin kunyar bambancin shekarun ba.
“A gaskiya, ban lura da shi ba. Kuma kodayake akwai shekaru 45 a tsakaninmu, ina tafiya tare da ita ko’ina.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Adrián Narbáez
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisa ta amince da karatu na biyu kan ƙirƙirar sabbin Jihohi 4
Majalisar Wakilai ta ɗauki mataki na gaba wajen ƙirƙirar sabbin jihohi huɗu a Najeriya.
’Yan majalisa sun tattauna tare da amincewa da karatu na biyu na ƙudirorin da ke neman kafa jihohin Oke-Ogun, Ijebu, Ife-Ijesa, Tiga, Orlu, da Etiti.
Gidauniyar Daily Trust da WRAPA sun ’yanta fursunoni 21 a Kaduna da Katsina Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdullahi Usman, ya rasuWaɗannan ƙudirori na daga cikin yunƙurin sauya kundin tsarin mulkin 1999.
Shugaban masu rinjaye na majalisa, Hon. Julius Ihonvbere, wanda ya gabatar da ƙudirorin, ya jaddada muhimmancinsu.
“Waɗannan ƙudirori suna nuna buƙatun yankuna daban-daban na ƙasa domin samar da ingantaccen shugabanci da rarraba albarkatu cikin adalci,” in ji shi.
Mataimakin Kakakin Majalisa, Benjamin Kalu, wanda ya jagoranci zaman, ya jagoranci kaɗa ƙuri’ar murya inda ƙudirorin suka samu amincewa.
An tura su zuwa kwamitin majalisa kan sauya kundin tsarin mulki domin ci gaba da nazari.
Ɗaya daga cikin masu ɗaukar nauyin ƙudirin, Hon. Ghali Mustapha Tijani, ya ce, “Kafa Jihar Tiga zai kusanto da gwamnati ga jama’a tare da haɓaka ci gaba.”
Ana buƙatar amincewar majalisun dokokin jihohi da na ƙasa kafin ƙirƙirar sabbin jihohin a Najeriya.