Za a kafa ƙarin makarantu a Zariya — Abbas Tajudeen
Published: 23rd, February 2025 GMT
Shugaban Majalisar Wakilai, Dokta Abbas Tajudeen ya ce Kasafin Kuɗin Nijeriya na baɗi zai ba da damar kafa ƙarin makarantu na matakin Tarayya a mazaɓarsa ta Zariya.
Shugaban majalisar ya bayyana haka ne lokacin babban taron shekara-shekara karo na 31 da 32 na ƙungiyar bunkasa ilimi ta Zariya, watau ZEDA da aka gudanar a Zariya.
Ya bayyana cewa makarantun da ake shirin kafa wa sun haɗa da makarantar firamare da sakandare na yara masu buƙata ta musamman da kwalejin tarayya na koyon aikin noma da kiwo.
Shugaban majalisar ya kuma bayyana fara bada tallafin na musamman ga ɗaliɓin da ya fi kowa kwazo a fannin koyon ilimin kwamfuta da kuma ɗalibin da ya fi kowa nuna hazaƙa a bangaren makarantun sakandare da ke larɗin Zazzau.
Ya bayyana rashin jin daɗi bisa jinkirin da aka samu wajen biyan ɗalibai 2500 kuɗin tallafin karatu da suke lardin Zazzau, yana mai cewa za a ƙara yawan ɗaliban da za su riƙa cin moriya tallafin zuwa 3000 a shekarar 2026.
Shugaban majalisar ya ɗora alhakin jinkirin da aka samu wajen biyan tallafin akan kaddamar da kasafin kuɗin shekarar 2024, inda ya bayyana cewa za a biya kuɗin da zarar al’amura sun daidaita.
Haka kuma, ya ba da sanarwar cewa zai gina wa ƙungiyar ZEDA tare da sanya kayayyaki irin na zamani a ɗakin taro da zai ɗauki kimanin mutane dubu ɗaya.
Shugaban majalisar ya ƙara da cewa kudurin majalisar ne ganin ta bunkasa ilimi a matakin farko da inganta ilimin sakandare da na kimiyya da kawo sauyi a fannonin ƙirƙira.
Ya buƙaci kungiyar ZEDA da ta ɓullo da wani tsari da zai samar da yanayin bai wa malamai horo da shigar da iyaye cikin harkokin tattauna batutuwan da suka shafi ilimi.
Tun farko a jawabinsa na maraba, shugaban kwamitin tsare-tsare na kungiyar ta ZEDA, Dokta Abdul Alimi Bello ya ce kungiyar ta sami gagarumar nasara da ya nuna aniyar ta na samar da ingantaccen ilimi da bunƙasa al’umma.
Ya ce cikin shekaru da dama, ƙungiyar ta kasance jagoran kungiyoyi masu zaman kansu a lardin Zazzau da suke kula da ilimin zamani da bunkasa sana’o’in hannu.
A nasa jawabin, mai martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya buƙaci ƙungiyar da ta yi amfani da kuɗaɗen shigar ta wajen tabbatar da samar da kyakkyawan sauyi a ɓangaren ilimi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: makarantu Zariya Shugaban majalisar ya
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan
Hukumar kula da agaji ta MDD (OCHA) ta bada sanarwan cewa, gwamnatin HKI a yankin yamma da kogin Jordan ta kori Falasdinawa a gidaje 5 a yankin bayan sun rusa gidajensu. Hukumar ta kara da cewa wadanda HKI ta rusa gidajensu a yankin sun hada da yara 19 da da iyayensu 33 maza da mata 6.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto OCHA na cewa tun watan Maris da ya gabata zuwa yanzu, HKI ta rusa gidaje da gine-ginen Fafalsadinawa kimani 100 a yankin yamma da kogin Jordan wadanda suka hada da gabacin birnin Qudus da kuma sauran yankuna, da sunan an gina gidajen ba bisa ka’ida ba.
Banda haka suna kwace gonakin Falasdinawa don ginawa sabin yahudawan da suke shigowa kasar matsugunai.
Labarin y ace, a wasu lokutan yahudawan zasu tilastawa Falasdinawa rusa gidajensu da kansu ko kuma idan sun rusa su da kayan aikinsu su tilastawa Falasdinawan kbiyan kudaden aikin rusawan.