Aminiya:
2025-03-25@20:06:56 GMT

Za a kafa ƙarin makarantu a Zariya — Abbas Tajudeen

Published: 23rd, February 2025 GMT

Shugaban Majalisar Wakilai, Dokta Abbas Tajudeen ya ce Kasafin Kuɗin Nijeriya na baɗi zai ba da damar kafa ƙarin makarantu na matakin Tarayya a mazaɓarsa ta Zariya.

Shugaban majalisar ya bayyana haka ne lokacin babban taron shekara-shekara karo na 31 da 32 na ƙungiyar bunkasa ilimi ta Zariya, watau ZEDA da aka gudanar a Zariya.

Mai Pataskum ya buɗe masallacin garin Danga a Yobe An kama mutum biyu kan kisan wata mata saboda maita

Ya bayyana cewa makarantun da ake shirin kafa wa sun haɗa da makarantar firamare da sakandare na yara masu buƙata ta musamman da kwalejin tarayya na koyon aikin noma da kiwo.

Shugaban majalisar ya kuma bayyana fara bada tallafin na musamman ga ɗaliɓin da ya fi kowa kwazo a fannin koyon ilimin kwamfuta da kuma ɗalibin da ya fi kowa nuna hazaƙa a bangaren makarantun sakandare da ke larɗin Zazzau.

Ya bayyana rashin jin daɗi bisa jinkirin da aka samu wajen biyan ɗalibai 2500 kuɗin tallafin karatu da suke lardin Zazzau, yana mai cewa za a ƙara yawan ɗaliban da za su riƙa cin moriya tallafin zuwa 3000 a shekarar 2026.

Shugaban majalisar ya ɗora alhakin jinkirin da aka samu wajen biyan tallafin akan kaddamar da kasafin kuɗin shekarar 2024, inda ya bayyana cewa za a biya kuɗin da zarar al’amura sun daidaita.

Haka kuma, ya ba da sanarwar cewa zai gina wa ƙungiyar ZEDA tare da sanya kayayyaki irin na zamani a ɗakin taro da zai ɗauki kimanin mutane dubu ɗaya.

Shugaban majalisar ya ƙara da cewa kudurin majalisar ne ganin ta bunkasa ilimi a matakin farko da inganta ilimin sakandare da na kimiyya da kawo sauyi a fannonin ƙirƙira.

Ya buƙaci kungiyar ZEDA da ta ɓullo da wani tsari da zai samar da yanayin bai wa malamai horo da shigar da iyaye cikin harkokin tattauna batutuwan da suka shafi ilimi.

Tun farko a jawabinsa na maraba, shugaban kwamitin tsare-tsare na kungiyar ta ZEDA, Dokta Abdul Alimi Bello ya ce kungiyar ta sami gagarumar nasara da ya nuna aniyar ta na samar da ingantaccen ilimi da bunƙasa al’umma.

Ya ce cikin shekaru da dama, ƙungiyar ta kasance jagoran kungiyoyi masu zaman kansu a lardin Zazzau da suke kula da ilimin zamani da bunkasa sana’o’in hannu.

A nasa jawabin, mai martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya buƙaci ƙungiyar da ta yi amfani da kuɗaɗen shigar ta wajen tabbatar da samar da kyakkyawan sauyi a ɓangaren ilimi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: makarantu Zariya Shugaban majalisar ya

এছাড়াও পড়ুন:

SDP: Ba Mu Yi Wa Kowa Alƙawarin Takarar Shugaban Ƙasa Ba

“SDP jam’iyya ce mai zaman kanta, kuma za mu ci gaba da bin tsarukanmu da dokokinmu wajen zaɓen ‘yan takara,” in ji shi.

“Za Mu Fi Mayar da Hankali Kan Ci Gaban Jama’a”

Shugaban jam’iyyar ya bayyana damuwa kan halin da ‘yan Nijeriya ke ciki, musamman matsalar tsadar rayuwa da rashin tsaro.

Ya ce SDP ba za ta zama mafakar wasu ‘yan siyasa masu neman mulki ba tare da wani ingantaccen shiri ba.

“Dole mu duba halin da ƙasa ke ciki. Tsadar rayuwa na ci gaba da ƙaruwa, mutane na fama da wahala, amma ana cewa tattalin arziki yana inganta. Dole ne a fuskanci gaskiya, a yi aiki don ci gaban jama’a, ba kawai neman mulki ba,” in ji Gabam.

SDP Na Ci Gaba da Ƙarfafa Tsarukanta

Ya ce jam’iyyar na shirin fitar da manufofi masu amfani ga al’umma, inda za ta ba da dama ga matasa da mata wajen shiga siyasa da kuma samar da sabbin shugabanni masu nagarta.

Wannan furuci na shugabannin SDP na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta raɗe-raɗin cewa wasu manyan ‘yan siyasa na shirin shiga jam’iyyar don samun damar takarar shugaban ƙasa.

Duk da haka, jam’iyyar ta bayyana cewa ba za ta sauya tsarinta domin kowanne mutum ba, kuma za ta bi ƙa’ida wajen fitar da ‘yan takara a zaɓen 2027.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Kafa Rundunar Daukin Gaggawa Don Magance Matsalolin Tsaro
  • NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi
  • SDP: Ba Mu Yi Wa Kowa Alƙawarin Takarar Shugaban Ƙasa Ba
  • Mutum 2,000 za su riƙa kamuwa da cutar HIV duk rana a duniya — MDD
  •  Jam’iyyar “Turkish National Party” Ta Tsaid Imam Uglu A Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa
  •  Shugaban Majalisar Dokokin Lebanon Ya Yi Gargadi Akan Masu Tunanin Kulla Alakar Kasar Da HKI
  • Ban bai wa majalisa haƙuri ba — Natasha
  • Fiye Da Dalibai 4,200 Suka Amfana Da Tallafin Ilimi Na Sanata Solomon Adeola
  • Moscow : Dole ne Rasha da China su shiga tattaunawar nukiliya da Iran