Gawuna ne ya lashe zaɓen Gwamnan Kano a 2023 — Ata
Published: 23rd, February 2025 GMT
Ƙaramin Ministan Gidaje da Tsara Birane, Yusuf Abdullahi Ata, ya bayyana cewa ɗan takarar Gwamnan Kano na jam’iyyar APC a Zaɓen 2023 Nasiru Yusuf Gawuna ne ya yi nasara.
Sai dai Ministan ya ce ƙaddarar hukunci daga Allah ne ya sanya a yanzu haka ba shi ke riƙe da madafan iko a Jihar Kanon ba.
Jami’ar Sojoji ta BIU ta ƙaddamar da taron magance zamba Za a kafa ƙarin makarantu a Zariya — Abbas TajudeenAta ya faɗi hakan ne yayin da yake barazanar ficewa daga jam’iyyar APC muddin ake sake naɗa Abdullahi Abbas a matsayin shugaban jam’iyyar na Jihar Kano.
Ministan ya ce kalaman da shugaban jam’iyyar ya riƙa furtawa su ne dalilin da Allah Ya ƙwace mulkin jihar daga hannun jam’iyyar duk da cewa ƙarara ita ce ta lashe zaɓen gwamnan jihar a shekarar 2023.
Aminiya ta ruwaito cewa furucin Ministan na zuwa yayin wani taron ƙusoshin jam’iyyar APC na Ƙaramar Hukumar Fagge da aka gudanar a Kano.
A cewarsa, “muna sake jaddada aniyar cewa idan suka dawo mana da shi [Abdullahi Abbas], za mu fice daga jam’iyyar.
“Saboda muddin haka ta kasance babu makawa sai jam’iyyar ta sake shan ƙasa. Ba ma tare da irin waɗannan mutane kuma ko mai za faru ba za mu yi tarayya da waɗannan mutanen ba.”
Ata ya bayyana kalaman da Abdullahi Abbas ya riƙa furtawa a matsayin dalilin da jam’iyyar APC a Kano ta sha ƙasa a Zaɓen 2023 — waɗanda ya bayyana a matsayin lafuza marasa kan gado kuma masu munana ladabi ga Allah.
Ya yi gargaɗin cewa muddin aka sake danƙa wa Abdullahi Abbas ragamar jagorancin jam’iyyar to babu makawa sai ta sake shan ƙasa.
“Mun taso an yi mana kyakkyawar tarbiyya, mun san wane ne Allah. Muna girmama malamai da manya saboda haka ba za mu sauka daga kan wannan tarbiyyar ba.
“Amma idan sun dage cewa lallai sai sun dawo da shi [Abdullahi Abbas], za mu fita mu ƙyale musu jam’iyyar kuma na rantse sai jam’iyyar ta sake faɗuwa.”
Minista Ata ya jaddada buƙatar sauya Abdullahi Abbas da wani jagora mai mutunci da daraja muddin jam’iyyar APC tana da burin samun nasara a Jihar Kano.
Kazalika, ya ce Allah ne Yake bayar da mulki ba tasirin yawan ƙuri’u ko dukiya ba.
“Kuri’u ko kuɗi ba sa bayar da mulki hakazalika mutane ba sa yanke hukunci kan wanda zai jagorance su saboda duk wannan lamari a hannun Allah yake.
“Gawuna ne ya yi nasara amma aka murɗe mana zaɓen. Muka garzaya kotu kuma ta tabbatar da cewa an yi mana maguɗi.
“Amma a ƙarshe wanda yake bayar da mulki ya karɓe daga hannunmu saboda ya nuna mana iyakarmu,” in ji Ata.
Wannan dai shi ne karon farko da Ministan ya fito ƙarara ya soki shugabancin jam’iyyar APC a Kano.
Sai dai ana danganta lamarin da yadda wasu ƙusoshin jam’iyyar ke adawa da naɗinsa a matsayin Minista bayan sauke Abdullahi Tijjani Gwarzo da Shugaba Bola Tinubu ya yi.
Bayanai sun ce gabanin zaɓen 2023 an
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Nasiru Yusuf Gawuna zaɓen 2023 jam iyyar APC
এছাড়াও পড়ুন:
Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
Tsangayar Ilimi na Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ya shirya wani taron bikin cika shekaru 50 da kafuwa tare da gudanar da taron kasa karo na uku.
Taron wanda aka yi wa take da “Ilimi Mai Sauya Rayuwa Don Gaba: Fuskantar Sabbin Kalubale da Buɗe Damar Samun Ci gaba” ya samu halartar manyan masu ruwa da tsaki daga sashen ilimi.
Da take jawabi a wajen taron, Minista a ma’aikatar Ilimi Farfesa Suwaiba Ahmed Sa’id ta bayyana cewa, a ƙoƙarin da gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu ke yi na ƙarfafa tsarin ilimi, ya amince da kashe Naira biliyan 120 don bunƙasa shirin fasaha da koyon sana’o’i (TVET) a Najeriya.
Ministar ta kuma bayyana cewa, gwamnatin tarayya ta amince da fitar da Naira biliyan 40 domin kammala aikin ɗakin karatu na ƙasa da aka yi watsi da shi, domin tallafawa bincike da cigaban karatu.
Farfesa Suwaiba ta ƙara da cewa, ma’aikatar ilimi ta tarayya ƙarƙashin jagorancin Minista Alausa ta ƙaddamar da Shirin Sabunta Hanyar Ilimi ta Najeriya (NESRI).
“Ina da burin mayar da Najeriya daga tattalin arzikin da ke dogara da albarkatu zuwa tattalin arzikin da ke dogara da ilimi, tare da rage yawan yara da ba sa zuwa makaranta, rage ƙarancin koyo, da samun ƙara ƙwarewa.”
Yayin da yake buɗe taron, Shugaban Jami’ar Bayero Kano, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya bayyana nasarorin da sashen ya samu, inda ya ce ya samar da manyan mutane kamar ministocin ilimi biyu, shugabannin jami’o’i tara, da matan gwamnan jihar Kano guda uku, da sauran fitattun ’yan Najeriya da suka yi fice a fannoni daban-daban.
Yayin da yake yabawa taken taron da dacewarsa, Farfesa Sagir ya tabbatar da cewa jami’ar tana nan daram wajen tallafawa duk wani shiri da zai ɗaga matsayin ilimi zuwa na ƙasa da ƙasa.
A jawabinsa na maraba, Shugaban tsangayar Ilimi na Jami’ar Bayero Kano (BUK), Dakta Abubakar Ibrahim Hassan, ya jaddada yadda tsangayar ke kokari wajen shirya harkokin ilimi da na kimiyya.
“Daga cikin nasarorin da Jami’ar BUK ta samu a kwanan nan akwai samun tallafin TETFUND guda biyu da kowanne ya haura naira biliyan 30, tare da lashe wani shirin koyar da harsuna biyu wanda Bankin Raya Musulunci da Hukumar Ilimin Firamare ta Kasa (UBEC) suka dauki nauyi.”
Taron ya yi armashi inda aka bayar da lambar yabo ga fitattun ‘yan Najeriya da suka hada da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, da matarsa Farfesa Hafsat, da Minista a ma’aikatar Ilimi ta Jiha Farfesa Suwaiba, tsohuwar Ministar Ilimi Farfesa Rukayya, da Farfesa Isah Yahaya Bunkure da wasu da dama.
Daga Khadija Aliyu