Aminiya:
2025-03-26@06:22:09 GMT

’Yan bindiga sun harbe fasto, sun sace wasu a coci

Published: 23rd, February 2025 GMT

’Yan bindiga sun kai hari wata coci da ke yankin Ogwashi-Uku a Jihar Delta, inda suka yi awon gaba da masu ibada a daren ranar Juma’a.

Sun harbi fasto sannan suka sace masu i ada shida a cocin, lamarin da ya jefa al’umma cikin firgici.

Gawuna ne ya lashe zaɓen Gwamnan Kano a 2023 — Ata Jami’ar Sojoji ta BIU ta ƙaddamar da taron magance zamba

Sun kai harin ne da misalin ƙarfe 10 na dare kusa da Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Delta.

Maharan sun harbi fasto, Apostle Divine Omodia, wanda yanzu haka yake kwance a asibiti.

Mutanen yankin suna cikin fargaba kan rashin tsaro a wuraren ibada, inda suke roƙon gwamnati ta ceto mutanen da aka sace tare da kama waɗanda suka kai harin.

Matar faston, Fasto Faith Omodia, ta bayyana jimaminta kan faruwar lamarin.

Ta ce ’yan bindigar sun buɗe wuta a cikin cocin.

“Na kwanta da jaririna a cikin coci sai na ji harbe-harbe. Kafin na ankara, harsasai sun fara shigowa cikin ɗakin da muke ciki.

“Ɗaya daga cikinsu ya harbe ni, amma harsashin bai shiga jikina ba. Sai dai kawai na ga wuta,” in ji ta.

Ta kuma ce an harbi mijinta a ƙafarsa, sannan ya rasa yatsu biyu.

Bayan haka, ’yan bindigar sun tattara masu ibada, tare da yin awon gaba da mutum shida, ciki har da masu gadin cocin biyu.

Mutanen da aka sace sun haɗa da Helen Onwuamaeze, Ariyo Emmanuel, Chike Okolo, da Blessing Waye, tare da masu gadi biyu da ba a bayyana sunayensu ba.

Rundunar ’yan sandan Jihar Delta ba ta tabbatar da faruwar harin ba tukuna.

Lokacin da aka tambayi kakakin rundunar, Bright Edafe, ya ce babu wani rahoto da aka kai ofishin ’yan sanda kan harin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindi6 harbi Jihar delta Mabiya Rauni

এছাড়াও পড়ুন:

Matasa Sun Daka Wawasu Kan Tirelar Kayan Agajin Ramadan Na Seyi Tinubu A Gombe 

Shirin ya fuskanci suka sosai a shafukan sada zumunta, inda suke ganin cewa, Arewa ta cancanci kulawa fiye da haka, yayin da wasu kuma ke ganin tallafin ya dace.

 

A wani faifan bidiyo da Daily Trust ta gani, an ga wasu fusatattun matasa suna kwashe kayan abinci a wata babbar mota da aka ajiye a bakin titi.

 

An ga matasan suna jefo kayan ga wadanda suke kasa domin tattarawa musu, sannan suka yi awon gaba da kayayyakin.

 

Abubuwan da ke cikin Tirelar sun haɗa da shinkafa, sukari, man girki, gishiri da taliya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu neman yi wa Natasha kiranye ba su cika ƙa’ida ba — INEC
  • Alamar Deepseek” Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya
  • Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe
  • ECOWAS Za Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • ‘Yansanda Sun Cafke Mutum 2 Kan Zargin Kashe Ɗan Achaɓa Da Sace Babur Ɗinsa A Bauchi 
  • Harin Neman Shahada Ya Kashe ‘Dan Share Wuri Zauna Daya A Garin Haifa
  • Matasa Sun Daka Wawasu Kan Tirelar Kayan Agajin Ramadan Na Seyi Tinubu A Gombe 
  • Ɗansanda Ya Kashe Matar Abokin Aikinsa, Ya Jikata Wasu Biyu A Ribas
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar