Wani kamfani dan kasar Saudiyya mai suna Mashariq Al Dhabia, ya rattaba hannu kan wata yarjejeniyar aiki aka yi wa kwaskwarima da hukumar Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) domin hidima ga Alhazan Nijeriya a lokacin aikin Hajjin 2025. LEADERSHIP ta rahoto cewa, kamfanin a baya ya yi barazanar maka NAHCON a kotu bisa zargin karya sharudan kwangilar da hukumar ta rattaba wa hannu kan hidima ga Alhazan Nijeriya a Masha’ir a lokacin aikin Hajjin 2025.

Al’ummar Katsina Sun Koka Da Taɓarɓarewar Hanya Da Ƙarancin Ruwan Sha Al’ummar Katsina Sun Koka Da Taɓarɓarewar Hanya Da Ƙarancin Ruwan Sha Amma a wani al’amari mai ban mamaki, sai aka hangi wata tawaga daga kamfanin na Saudiyya a karkashin jagorancin shugaban kamfanin, Muhammad Hassan, ta ziyarci babban ofishin hukumar ta NAHCON da ke ‘Hajji House’ a Abuja ranar ranar Asabar, 22 ga watan Yuli, domin rattaba hannu kan yarjejeniyar kwangilar da aka sabunta. Da yake jawabi bayan rattaba hannun, shugaban hukumar ta NAHCON, Farfesa Abdullahi Seleh Usman, ya bayyana cewa, sabunta yarjejeniyar ya zama dole domin  gyara wuraren da aka samu kuskuren fahimta da kuma tabbatar da gudanar da ayyukan hajji cikin sauki da samun nasara. Ya kuma tabbatar wa da dukkan maniyyatan Nijeriya cewa, NAHCON ta kammala shirye-shiryenta, tare da yin watsi da duk wata muguwar magana kan zargin soke kwangilar aikin. Muhammad Hassan, shugaban Mashariq Al Dhabia, ya bayyana godiyarsa ga NAHCON tare da bayar da tabbacin yin hidima ƙayatacciya ga Alhazan Nijeriya.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar “Gulani” Ta Shiga Sahun Masu Kin Amincewa Da Yaki

A kalla tsoffin sojojin rundunar “Gulani” ta HKI 150 ne su ka rattaba hannu akan takardar yin kira da a dawo da fursunoni gida daga Gaza.

Ita dai rundunar “Gulani” ce mafi karf a tsakanin rudunonin sojan HKI,kuma tun da aka kafa ta, ta shiga dukkanin yake-yaken da HKI ta yi.

Wadanda su ka rattaba hannu akan wasikar sun bayyana goyon bayansu ga wasikar da sojan sama su ka rubuta a ranar 9 ga watan Aprilu da ake ciki,ko da kuwa sakamakon hakan shi ne kawo karshen yaki.

A cikin sa’o’i 48 da su ka gabata,dubban sojojin HKI sun rattaba hannu akan wasika wacce take yin kira da a kawo karshen yakin Gaza da kuma dawo da fursunonin da suke can.

A ranar juma’ar da ta gabata kafafen watsa labaru HKI sun ambaci cewa, da akwai sojojin bayan fage 1000 da su ka rattaba hannu akan wasika, da kuma tsofaffin sojojin soja a tsakaninsu da akwai wadanda suna kan ganiyar aikinsu.

Bayan wannan ne kuma sojojin dake kula da motocin yaki da tankoki su 15,25 su ka bi bayansu, sai kuma wasu tsoffin sojojin sama Jannati ,haka nan kuma sojan ruwa da likitocin soja 100. A cikin kwanaki  kadan da su ka gabata ma dai wasu jami’an daga cikin tsoffin ma’aikatan kungiyar leken asirin soja sun shiga cikin masu rubuta wasikar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabon Shugaban Kasar Gabon Ya Bayyana Shiransa Na Kawo Sauyi Mai Kyau A kasar
  • Rundunar “Gulani” Ta Shiga Sahun Masu Kin Amincewa Da Yaki
  • Gwamnatin Kebbi Za Ta Dauki Nauyin Karatun Dalibai A Saudiyya
  • Babban Daraktan Hukumar IAEA, Zai Ziyarci Iran ranar Laraba
  • Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • HKI Ta Jefa Boma-Bomai A Kan Asbiti Tilo Da Ya Rage Yake Aiki A Arewacin Gaza
  • Ta kai ƙarar kamfanin jirgi da fasinja kan kukan yaro
  • Shugaban Burkina Faso Ya Yi Fatali Da Tayin Saudiyya Na Gina Masallatai 200 A Kasarsa
  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo