Gwamnan ya gargadi jami’an gwamnati da su kauce wa dabi’ar nuna san kai da rashin gaskiya wajen zabo matan da za su amfana da wannan tallafi.

A cewar Gwamna Radda, an zabo mata 10 daga kowace guduma, kuma za a bai wa kowace mace awaki guda hudu da suka hada awaki uku da bunsuru daya, sannan za a bai wa kwararren manomi guda hamsin wanda zai koyar da su dubarun kiwo.

Tun da farko da take jawabi, kwaminisiyar harkokin mata ta Jihar Katsina, Hajiya Hadiza Yar’adua ta bayyana wannan tallafi a matsayin wata gagarumar gudummawa da gwamnati za ta bunkasa harkokin mata ta hanyar dogoro da kai.

A cewarta, taimakon da Gwamna Radda ya bayar ko shakka babu zai amfani mata masu sana’o’i tare bunkasa tattalin arziki a Jihar Katsina da ƙasa baki daya.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An kama mutum biyu kan kisan wata mata saboda maita

Rundunar ‘yan sandan yankin Biu ta tsare wasu mutane biyu da ake zargi da kashe wata mata ‘yar shekara 50 da ake zargi da bokanci da maita.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Borno, Yusuf Lawan ya tabbatar da hakan ga manema labarai a Maiduguri.

Ɗan shekara 43 ya auri mai shekara 88 Yadda ƙananan yara ke zaman kurkuku ba tare an da kai su kotu ba

Kwamishinan ya ce an kashe matar mai suna Hajara Saleh ne a ranar 21 ga watan Fabrairu a unguwar Bantine da ke Ƙaramar Hukumar Biu ta Jihar Borno.

Kwamishinan ya bayyana cewar, waɗanda ake zargin — Ja’o Muhammad da Idris Muhammad — sun yi tarayya wajen kashe matar a dalilin zargin maita da suke mata.

Lawan ya ce matar ta samu raunuka a wuyanta, kafafu, da hannayenta, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwarta.

Ya ce wani mazaunin unguwar Dadinkowa Gunda ne ya kai wa ’yan sanda rahoton faruwar lamarin da misalin karfe 11:00 na safiyar ranar.

“Da isa wurin da lamarin ya faru, jami’anmu sun gano cewa mijin nata Saleh Bole da sauran ‘yan uwa sun rigaya sun binne ta kamar yadda addinin musulunci ya tanada,” in ji kwamishinan.

Ya ƙara bayyana cewa, duk da jana’izar da aka yi wa matar amma jami’an ‘yan sanda sun yi nasarar ɗaukar hoton gawar marigayiyar tare da tattara muhimman shaidu.

Kwamishinan ya bayyana abin da ya faru a matsayin dabbanci da rashin gaskiya, yana mai gargaɗin cewa bai kamata a yi amfani da zargin maita a matsayin hujjar tashin hankali ko kisan gilla ba.

“Rundunar ‘yan sanda ta jajirce wajen gurfanar da duk wadanda suka aikata wannan danyen aiki a gaban kuliya.

“Don haka ya kamata jama’a su fahimci cewa doka ba ta ba mutane damar ɗaukar al’amura a hannunsu ba,” inji shi

A cewarsa, waɗanda ake zargin suna fuskantar tuhuma da suka haɗa baki, kisan kai, da sauran laifuka masu alaƙa da su, inda ya ce za a gurfanar da su gaban kuliya da zarar an kammala bincike.

Lawan ya buƙaci al’umma da su kai rahoton zargin bokanci ko duk wasu korafe-korafe ga ‘yan sanda maimakon ɗaukar doka a hannu.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cittar Da Ake Fitarwa kasashen Waje Ta Ragu Da Kashi 74 Cikin 100
  • An kama mutum biyu kan kisan wata mata saboda maita
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Wani Mutum Tare Da Sace Mutum Biyu A Kaduna
  • Yake-Yaken Kasa Da Kasa Ne Suka Mamaye Taron G20 Na Ministocin Harkokin Wajen Kungiyar A Afirka Ta Kudu
  • Abubuwan Sha Domin Ƙarin Ni’ima Ga Mata
  • Malamai Na Karbar Horo Akan Shirin Ilimin Mata Na AGILE a Jigawa
  • An tara Naira 16 a taron ƙaddamar da littafin IBB
  • Shirin Rigakafin Cututtuka Na UNICEF/GAVI Ya Sami Cikakken Hadin Kan Gwamnatin Jihar Jigawa
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Shirin Da’awah Na Mata A Jihar Jigawa