Amurka Ta Zama Jagorar Bata Ka’idoji Da Dokar Duniya Bisa Amfani Da Makamin Harajin Kwastam.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya

Shugaba hukumar makashin Nukliya na kasar Iran Mohammad Islami ya bada sanarwan cewa a ranar 8 ga watan Afrilu mai zuwa. Yace hukumarsa za ta kaddamar da sabbin magunguna da ta samar tare da amfani da makamashin Nukliya, a dai dai na ranar makamashin Nukliya ta kasar.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ta nakalto Islami yana fadar haka a yau Lahadi, ya kuma kara da cewa wannan ci gaban kari ne, kan ci gaban da kasar ta samu a wannan fannin, wanda kuma zai kara kyautata bangaren lafiya na kasar sannan ya zama hanyar samar da kudade ga kasar.

Shugaba hukumar makamashin nukliya ta Iran ya kara da cewa a cikin shekarar Iraniyawa wanda ya kara kadai kasar ta samar da sabbin ci gaba kimani 100 tare da amfani da makamashin nucliya, kuma tana son nan da shekara ta 2040 masana’antar makamashin nukliya ta kasar Iran zata shiga cikin masana’antun makamshin nukliya mafi girma a duniya.

Ana saran shugaba Pezeshkiyan zai halarci taron kaddamarda wadandan kayakin ci gaba da aka samu a ranar 8 ga watan Afrilu mai zuwa.

Sannan Iran ta dage kan cewa shirinta na makamashin Nukliya na zaman lafiya ne, sabanin abinda kasashen yamma musamman Amurka take zargin kasar na cewa shirin ya wuce na zaman lafiya.

Sai dai kakakin Fadar Krimlin na kasar Rasha Dmitry Medbedev ya bayyana a makon da ya gabata kan cewa shirin makamashin Nukliya na kasar Iran na zaman lafiya ne.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasuwar Kayayyakin Masarufi Ta Sin Za Ta Ci Gaba Da Nuna Yanayin Bunkasa Bisa Daidaito A Bana
  • Hamas : Isra’ila ta yi amfani da sulhu wajen tattara bayanai kan shugabannin Hamas domin kashe su
  • Mutum 2,000 za su riƙa kamuwa da cutar HIV duk rana a duniya — MDD
  • Sin Ta Sanar Da Dokar Dakile Takunkuman Kasashen Waje
  • Kiyaye Ci Gaba Mai Dorewa A Huldar Sin Da Amurka Ya Dace Da Moriyar Sasssan Biyu
  • Yawan Ziyarar Da ‘Yan Siyasa Da ‘Yan Kasuwar Amurka Ke Kawowa Sin Ya Zo Da Mamaki
  • Dokar Ta-ɓaci A Ribas: Gwamnonin PDP Sun Ƙalubalanci Hukuncin Tinubu A Kotun Ƙoli
  • Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas
  • Masanin Amurka: Matakan Kariyar Cinikayya Da Amurka Ke Aiwatarwa Babban Kuskure Ne
  • Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya