Matuƙar Abdullahi Abbas Ya Cigaba Da Zama Shugaban APC A Kano, Zan Fita – Ata
Published: 23rd, February 2025 GMT
Matuƙar Abdullahi Abbas Ya Cigaba Da Zama Shugaban APC A Kano, Zan Fita – Ata.
এছাড়াও পড়ুন:
Pezeshkian: Hadin gwiwar Iran da Saudiyya zai zama abin koyi ga dukkanin kasashen yankin
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce Jamhuriyar Musulunci ta Iran da Saudiyya za su iya zama abin koyi ga hadin gwiwar yankin, yana mai jaddada cewa hadin kan kasashen musulmi wani lamari ne da ake bukata don samun zaman lafiya, tsaro, da ci gaban tattalin arziki mai dorewa a yankin.
Pezeshkian ya bayyana hakan ne a yayin ganawa da ya yi da ministan tsaron kasar Saudiyya Yarima Khalid bin Salman da tawagarsa a birnin Tehran, bayan da ministan na Saudiyya ya isa babban birnin kasar Iran domin tattauna batutuwan da suka shafi yankin da alakar kasashen biyu.
Shugaban na Iran ya jaddada zurfafa dangantakar addini da al’adu da tarihi a tsakanin kasashen musulmi, yana mai jaddada wajabcin karfafa hadin kai a duniyar musulmi.
Shugabar kasar ta Iran ya ce: al’ummar Saudiyya ‘yan uwanmu ne, kuma tun farkon kama aikin gwamnatinmu, mun yi kokarin karfafa alakar ‘yan uwantaka a tsakanin dukkanin kasashen musulmi. Ya kara da cewa, idan kasashen musulmi suka cimma matsaya ta bai daya da hadin kai na hakika, to gwamnatin yahudawan sahyoniya ba za ta sake haifar da bala’i irin na kisan bil’adama a yankin ba kamar yadda suke yi yanzu a zirin Gaza.
Ya kuma tabo batun muhimmancin ajiye bambance-bambance a gefe, da inganta hadin gwiwa a yankin.
Pezeshkian ya jaddada cewa, “Shugabannin kasashen musulmi za su iya yin aiki tare, kuma su gabatar da wani abin koyi na rayuwa tare, da wadata, da ci gaba ga sauran al’ummomi na duniya.
Ya kuma yaba da ra’ayin kafa kungiyoyin aiki na hadin gwiwa a bangarori daban-daban na siyasa, tattalin arziki da tsaro tsakanin Iran da Saudiyya.