Matuƙar Abdullahi Abbas Ya Cigaba Da Zama Shugaban APC A Kano, Zan Fita – Ata.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ana barazanar korar sojojin Isra’ila da ke neman a kawo ƙarshen yaƙin Gaza

Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya yi barazanar korar sojojin da ke neman kawo karshen yakin Gaza bayan sun rattaba hannu kan wasu takardu da ke nuna bukatar hakan.

A bayan nan dai fiye da sojoji 1,500 na rundunar da ke kula da tankokin yaƙi ta Isra’ila, ciki har da janar-janar, suka sanya hannu kan wata takardar neman gwamnatin Isra’ila ta mayar da hankali kan dawo da waɗanda aka yi garkuwa da su a Gaza, ko da hakan zai kai ga dakatar da yaƙin da ake yi a yankin Falasdinawa.

Budurwar da ke rayuwa a banɗaki don gudun biyan kuɗin hayar gida HOTUNA: Zulum ya karɓi baƙuncin Majalisar Sarakunan Arewa a Borno

A cewar Jaridar Maariv a ranar Litinin, sojoji 1,525 daga rundunar tankokin sun sanya hannu kan wannan takardar, daga masu ɗauke bindiga har zuwa janar-janar.

Sun bukaci gwamnati “ta yi duk mai yiwuwa don tabbatar da an sako wadanda aka yi garkuwa da su — ko da hakan zai kai ga dakatar da yakin.”

Waɗanda suka sanya hannun sun hada da sojojin da suka yi aiki a rundunar kula da tankoki sannan suka koma rayuwar farar hula ba tare da zuwa makarantar jami’ai ba da tsofaffin sojoji da ƙananan kwamandoji, da kuma tsofaffin manyan jami’an sojin Isra’ila, ciki har da tsoffin shugabannin rundunar tankoki da kwamandojin sassa, kamar yadda Maariv ta bayyana.

Sunayen masu sanya hannu sun hada da tsohon Firaminista kuma tsohon shugaban sojoji Ehud Barak da tsohon shugaban rundunar tsakiya Amram Mitzna da tsohon shugaban hafsoshin tsaro Dan Halutz da tsohon shugaban leƙen asiri na soja Amos Malka da tsohon shugaban rundunar tsakiya Avi Mizrahi, da kuma tsohon kwamandan rundunar tankoki ta 14 Amnon Reshef.

Wannan takardar buƙatar ta kasance wani bangare na wani babban kira daga sojoji na yanzu da tsoffin sojojin Isra’ila da ke neman a dawo da wadanda aka yi garkuwa da su tare da kawo karshen yakin.

Tun daga ranar Alhamis, an fitar da kusan takardu goma daga sojoji da ke neman a kawo karshen yakin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Makasudin Rubuta Sakon Jagora Ga Shugaban Kasar Rasha
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar sun sasanta
  • Ministan harkokin wajen Najeriya Ya kai ziyara Nijar
  • Jigawa Za Ta Zama Cibiyar Binciken Lafiya Nan Ba Da Jimawa Ba – Gwamna Namadi
  • Ina Da Ƙwarewar Da Zan Iya Zama Shugaban Ƙasar Nijeriya – Makinde
  • Kotu ta yanke wa tsohon Shugaban Peru ɗaurin shekaru 15 kan laifin rashawa
  • Kotu ta yanke wa tsohon Shugaban Peru ɗaurin shekaru 15
  • Samarwa Matasa Abun Yi Shi Zai Kawo Ƙarshen Ta’addancin Boko Haram Da ‘Yan Bindiga – Zulum 
  • Ana barazanar korar sojojin Isra’ila da ke neman a kawo ƙarshen yaƙin Gaza
  • Sabon Shugaban Kasar Gabon Ya Bayyana Shiransa Na Kawo Sauyi Mai Kyau A kasar