Cittar Da Ake Fitarwa kasashen Waje Ta Ragu Da Kashi 74 Cikin 100
Published: 23rd, February 2025 GMT
dimbin Asarar Da Manoman Cittta Suka Tabka:
Shugabar kungiyar manoman Citta da sarrafata ta kasa (GGPMAN) Florence Edwards, ta alakanta samun raguwar Cittar da ake fitarwa daga kasar nan zuwa kasashen ketare da barkewar cutar da ta lalata gonakin wasu manomanta.
Florence ta kara da cewa, akasarin irin samfurin Cittar da manoman ke shukawa a fadin kasar nan, sun shafe sama da shekaru 20 suna amfani da shi.
Ita ma wata manomiyar Cittar a Jihar Kaduna, Joy Bolus ta bayyana cewa, ta kashe sama da Naira miliyan daya a shekarar da ta gabata wajen aikin noman Cittar a tata gonar, ta hanyar yin hadaka da miinta, amma saboda barkewar cutar a bara, hakan ya jawo gonar ta lalace baki-daya.
“A kakar noman bara, ni da mijina mun yi asarar sama da Naira 800, 000, bayan barkewar cutar”, a cewar Joy.
Duk kokarin da gwamnatin tarayya ta yi na magance yaduwar cutar, hakan bai samar da wani sakamako na a zo a gani ba, musamman ganin yadda manomanta a Jihohin Kaduna, Kano da wasu yankuna biyu na kasar da aka fi yin noman ke ci gaba da kirgar irn asarar da suka tabka sakamakon barkewar cutar.
karamin Ministan Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Sabi Abdullahi ya bayyana cewa, tun bayan barkewar cutar a 2023, manoman da annobar cutar ta afkawa a gonakinsu, sun yi asarar kimanin Naira biliyan 12.
A watan Oktoban 2023, gwamnatin tarayya; ta samar wa da manoman, musamman na jihohin da aka fi yin nomanta tallafin Naira biliyan 1.6 tare kuma da raba musu magungunan feshin cutar, domin rage musu radadin annobar.
Jaridar BusinessDay, tun da farko ta ruwaito cewa, farashin Cittar ya karu da rubi shida a shekaru biyu da suka gabata, inda kowane buhunta daya a 2023 ya kai Naira 50, 000, sannan kuma ya karu zuwa Naira 300,000 a shekarar 2025.
Wasu manoman, sun alakanta hauhawar farashin da barkewar cutar a 2023, inda hakan ya jawo wa manoman nata yin asarar kimanin Naira biliyan 12.
A cikin kasafin kudi na 2025, an kara wa Hukumar Samar da Ingantaccen Irin Noma ta kasa (NASC) kashi 36, kimanin Naira biliyan 3.8, sabanin Naira biliyan 2.8 da aka ware mata a kasafin kudi na 2024, amma abin takaici; har yanzu manoman kasar, ba su iya samun ingantaccen Irin ba.
A cewar Hukumar Samar Wadattacen Abinci da Bunkasa Aikin Noma (FAO) ta duniya ta ce, a fidin duniya kaf; Nijeriya na daya daga cikin kasashen da ke kan gaba wajen noman Citta, duba da yadda kasar ta noma kimanin tan 781,000 a 2023.
Mafi akasari, Nijeriya na fitar da Cittar da aka noma a kasar ne zuwa kasuwannin Gabas ta Tsakiya ko kuma Nahiyar Turai.
“Manoman Citttar, na bukatar samar musu da Irinta, mai bijer wa kowace irin cutar da ke yi wa gonakinsu illa tare kuma da yin gwajin kasar da ake noma ta, don gano inda cutar ke fara kunno kai”, in ji Florence.
এছাড়াও পড়ুন:
Araghchi : Ya kamata Duniyar Musulmi ta dauki mataki mai karfi kan Isra’ila
Ministan harkokin wajen kasar Iran, Abbas Araghchi, ya yi kakkausar suka kan zaluncin da gwamnatin Isra’ila ke yi kan al’ummar Falasdinu da ba su da kariya a yankin Zirin Gaza, yana mai jaddada bukatar hadin kai da daukar matakin gaggawa na kasashen musulmi domin dakile wadannan laifuka.
Babban jami’in diflomasiyyar ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan a ranar Asabar, inda ya bukaci kasashen musulmi a duk fadin duniya da su dauki kwararen matakai da hadin kai don tunkarar ta’addancin Isra’ila.
Araghchi ya yi nuni da yadda gwamnatin Isra’ila ta sake dawo da yakin da take yi na kisan kare dangi a kan Gaza tun ranar Talatar data gabata wanda ya keta yarjejeniyar tsagaita bude wutar da aka cimma a zirin.
Sabon farmakin Isra’ila ya yi sanadin mutuwar Falasdinawa sama da 1,000, akasari mata da yara, baya ga kusan mutane 48,000 da sojojin suka yi wa kisan kare dangi tun da farko.
A wani bangare na jawabin nasa, Araghchi ya yi tir da hare-haren wuce gona da iri da Amurka da Birtaniya ke yi kan kasar Yemen, inda ya bayyana irin asarar da aka yi a tsakanin mata da kananan yara da ba su ji ba ba su gani ba, da kuma lalata kayayyakin more rayuwa na kasar.
Ya jaddada nauyin daya rataya a wuyan al’ummar musulmin duniya na tallafa wa ‘yan uwansu a wannan kasa ta Larabawa mai fama da tashe-tashen hankula da talauci.
A nasa bangaren, Yarima Farhan ya nanata matsayar Riyadh na yin Allah wadai da mummunan zaluncin gwamnatin Isra’ila, Ya kuma jaddada wajabcin hada kai da hadin gwiwa a tsakanin kasashen yankin don hana barkewar rikicin.