HausaTv:
2025-04-15@15:35:02 GMT

Wakilin Jagoran Juyi A Wurin Jana’izar Sayyid: Gwgawarmaya Za Ta Ci Gaba

Published: 23rd, February 2025 GMT

Wanda ya wakilci jagoran juyin juya halin musulunci na Iran a wajen jana’izar Babban magatakardar kungiyar Hizbullah Sayyid Hassan Nasrallah da kuma Shahid Safiyuddin Hashim, ya gabatar da jawabi da a ciki ya bayyana cewa: Jagoran jihadi mai girma, kuma shugaban gwgawarmaya a cikin wannan yankin, Sayyid Hassan Nasrallah ( Allah ya daukaka matsayinsa)  ya kai matsayi na koli na daukaka da izza.

Sayyid Mujtaba al-Husainy ya kuma ce; A wannan lokacin za a binne gangar jikin Sayyid a cikin kasar da ya yi jihadi saboda Allah akanta, amma ruhinsa da kuma tafarkinsa na gwgararmaya zai kara daukaka fiye da kowane lokaci a baya.

Sayyid Mujtaba al-Husaini ya kuma ce:Makiya su kwana da sanin cewa, gwgawarmaya za ta cigaba da wanzuwa domin fuskantar zalunci da girman kai na duniya, ba kuma za ta karaya ba har sai an cimma manufa, da izinin Allah.”

Da yake Magana akan Sayyid Hashim Safiyuddin ( Yardar Allah a gare shi) ya bayyana shi a matsayin wani daga cikin taurari masu haske a cikin tarihin wannan yankin. Ya kuma kasance mataimaki mai tsarkin zuciya ga Sayyid Hassan Nasrallah.

A karshe Sayyid  Mujtaba al-Husaini ya yi addu’a ga wadannan shahidan biyu masu  girma da kuma sauran mujahidai da  dukkanin shahidai.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran

Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya bayyana alhininsa akan rasuwar Dr. Akbar I’itimadi wanda shi ne na farko da ya kafa hukumar makamashin Nukiliya ta Iran.

Wasikar ta’aziyyar da shugaban kasa ta kunsa ta ambaci cewa:  Shakka babu hidima mai kima da wannan masanin ya yi, ya share fagen gina da ci gaban fasahar makamashin Nukiliya a Iran da kuma mayar da kasar mai cin gashin kanta a wannan fage.

Har ila yau, shugaban kasar ta Iran ya mika sakon ta’aziyyarsa ga masana na Iran, da kuma iyalansa. Ya kuma yi addu’a da rokon Allah madaukin sarki da ya lullube shi da rahamarsa da kuma gafararsa, sannan ya bai wa iyalansa na hakuri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano Za Ta Sake Buɗe Makarantun Kwana 10 Don Inganta Ilimin Yara Mata
  • Kokarin Da Iran Take A Tattaunawa Da Amurka Shi Ne Dage Mata Takunkuman Zaluncin Da Aka Dora Mata
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 109
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato
  • Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran
  • ‘Yansanda Sun Gano Haramtaccen Wurin Hada Makamai A Kano
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Makiya Suna Hasadan Ci Gaban Kasar Iran
  • Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari
  • Sharhi: Tattaunawa Zagaye Na Farko Tsakanin Iran Da Amurka A Oman
  • Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?