Wakilin Jagoran Juyi A Wurin Jana’izar Sayyid: Gwgawarmaya Za Ta Ci Gaba
Published: 23rd, February 2025 GMT
Wanda ya wakilci jagoran juyin juya halin musulunci na Iran a wajen jana’izar Babban magatakardar kungiyar Hizbullah Sayyid Hassan Nasrallah da kuma Shahid Safiyuddin Hashim, ya gabatar da jawabi da a ciki ya bayyana cewa: Jagoran jihadi mai girma, kuma shugaban gwgawarmaya a cikin wannan yankin, Sayyid Hassan Nasrallah ( Allah ya daukaka matsayinsa) ya kai matsayi na koli na daukaka da izza.
Sayyid Mujtaba al-Husainy ya kuma ce; A wannan lokacin za a binne gangar jikin Sayyid a cikin kasar da ya yi jihadi saboda Allah akanta, amma ruhinsa da kuma tafarkinsa na gwgararmaya zai kara daukaka fiye da kowane lokaci a baya.
Sayyid Mujtaba al-Husaini ya kuma ce:Makiya su kwana da sanin cewa, gwgawarmaya za ta cigaba da wanzuwa domin fuskantar zalunci da girman kai na duniya, ba kuma za ta karaya ba har sai an cimma manufa, da izinin Allah.”
Da yake Magana akan Sayyid Hashim Safiyuddin ( Yardar Allah a gare shi) ya bayyana shi a matsayin wani daga cikin taurari masu haske a cikin tarihin wannan yankin. Ya kuma kasance mataimaki mai tsarkin zuciya ga Sayyid Hassan Nasrallah.
A karshe Sayyid Mujtaba al-Husaini ya yi addu’a ga wadannan shahidan biyu masu girma da kuma sauran mujahidai da dukkanin shahidai.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sadaukantaka, Kunya Da Kawar Da Kai Na Annabi Muhammadu (SAW)
Annabi (SAW) yana da Alfadarai Bakwai, akwai wazanda ya rike har ya rasu suna wurinsa akwai kuma wazanda ya bai wa wasu daga cikin sahabbansa. Wacce ya je yakin Hunaini da ita, wani sarkin Larabawa (zan makafatul kinani) ne ya bashi, akwai wacce sarkin Ailatu ya bashi akwai ta sarkin Limatul Jandali, akwai ta Sarki Najjashi, akwai ta sarkin Kisra, akwai ta sarkin Mukaukisu akwai Jindilu. Jindilu itace mashhuriya wacce Annabi ya rasu ya bar ta Sayyidina Aliyu ya ci gaba da hawanta, duk yakukuwan Sayyidina Ali, mafi yawancinsu a kanta ya yi, ranar yakin Wak’atu Jamal, Sayyada A’isha (RA) ta ganshi a kanta, sai ta ce “ya yi kama da zan’uwansa” sai mai rike da akalar rakuminta ya jefar ya koma cikin rundunar Sayyadina Ali ya ce masa, Sayyada tace “ka yi kama da zan’uwanka (Sayyadina Rasulallah).
Imam Muslim ya ruwaito Hadisi daga Abbas yana cewa “yayin da tawagar Musulmai da Kafirai suka hazu, sai Musulmai suka gudu suka juya baya, sai Manzon Allah shi kuma ya kasance yana jan alfadarinsa inda Kafiran suke, ni kuma ina rike da linzamin alfadarinsa ina jan linzamin baya shi kuma Abu Sufyan zan Haris zan Abdulmuzallib yana rike da wurin sanya kafafuwa na shimfizar alfadarin, sannan Annabi (SAW) ya yi kira ga Musulmai suka dawo.” A wata ruwaya kuma, Annabi (SAW), Baffansa Abbas ya sa ya kira Musulmai.
Annabi (SAW) ya kasance idan ya yi fushi (shi kuma ba ya fushi sai in an taba Allah), to wani abu bai iya tare shi, ko Sahabi ko tsoro ko wata razana.
Abdullahi zan Umar ya ce, “ban taba ganin wani abu mafi sadaukantaka ko karfin zuciya ko kyauta mafi yarda wanda ya fi Annabi (SAW) ba.”
Sayyadina Ali yana cewa “Mun kasance in yaki ya yi zafi, ya yi tsanani idanuwa suka sauya kala suka yi ja, sai mu dinga kare kanmu da Annabi (SAW), babu wani da yake kusantar makiya sai shi, sannan mu biyo bayansa.
An karbo Hadisi daga Anas yana cewa “Manzon Allah (SAW) ya kasance mafi kyawun Mutane, mafi kyautar mutane, mafi sadaukantakar mutane.”
Wata rana da dare mutanen Madina sun razana sabida kara mai karfi da aka ji ta taso a daren, Sahabbai suka fara bi gida-gida suna taso abokansu a je a duba sabida a san me ke faruwa. Kawai sai suka hazu da Manzon Allah (SAW) yana dawowa, ya riga su zuwa wurin, sabida sauri a dokin Abi Dalhata ya je kuma babu shimfiza a kan dokin, yana rataye da takobi yana cewa Sahabbai “kar ku tsorata, na je na gani babu komai.”
A wannan lokaci Madina ta kasance kullum ana tsoron wani daga cikin Sarakunan makiya zai kawo hari.
Imran bin Hussaini yake cewa, Manzon Allah (SAW) bai taba hazuwa da wata runduna ba sai ya kasance na farko wanda zai fara kai musu hari.
Yayin da Ubayyu bin Khalaf ya ga Annabi (SAW) a ranar yakin Uhudu, Ubayyu ya fito yana cewa, Ina Muhammadu yau sai zaya ya mutu a cikinmu, ko ni ko shi. Ubayyu yana daga cikin wazanda suka fanshi kansu a ranar yakin Badr, bayan ya fanshi kanshi sai ya ce wa Annabi (SAW), yana da doki da ya kulle kullum yana bashi masaki na dawa, a kansa zan kashe ka, sai Manzon Allah (SAW) ya ce masa, Insha Allah, ni ne zan kashe ka a kanshi. A ranar yakin Uhudu da Ubayyu ya ga Annabi (SAW), sai ya sukwano dokinshi zuwa ga Annabi (SAW), Mazaje sadaukai suka yi kanshi sai (SAW) ya ce musu “ku kyale shi haka nake so”. Sai Manzon Allah (SAW) ya karbi wani mashi a hannun wani sahabi sannan ya soke shi a wuya daga kan dokinshi, sai ya koma yana ce wa kuraishawa, Muhammadu ya kashe ni, an ruwaito cewa, Ubayyu ya Mutu a hanyar dawowarsa daga Uhudu zuwa Makkah.
Kunya Da Kawar Da Kai Na Manzon Allah (SAW)
Wannan kazan kenan daga cikin sadaukantaka irin ta Annabi (SAW), yanzun kuma za mu juya akalar karatunmu zuwa ambaton wasu daga cikin halayen Kunya da kawar da kai na Manzon Allah (SAW).
Abin da ake nufi da kunya shi ne taushin zuciya da yake bijirowa a fuskar zan Adam yayin da mutum ya aikata wani aiki ko ya faza wata magana da ake kin ji ko gani, ko kuma mutum ya aika ta abin da rashin aikata shi ya fi, sai zan Adam ya ce “ina ma na bari ban aikata ba.”
Shi kuma runtse ido ko kawar da kai, yana nufin rafkana da abin da mutum ba ya so a aikata masa (ba ya so a aikata masa wani abu, ga kuma wani ya nace sai ya aikata abin da ba a son) shi kuma sai ya kawar da kai ya nuna bai san ma ana yi ba.
Manzon Allah (SAW) ya fi kowa Kunya sabida Hadisin “Alhaya’u minal Iman… – Kunya tana daga cikin Imani”.
Manzon Allah (SAW) yana cewa, “wanda bai da kunya, ya aikata abin da ya ga dama, Allah ba ruwanshi da shi”. Annabi (SAW) shi ne mafi kawar da kai ga Al’aurar Mutane.
Ubangiji tabaraka wata’ala ya faza cikin kur’ani “Ya ayyuhallazina amanu la tadkhulu buyutan nabiyya illa an yu’uzana lakum ila za’amin gaira nazirina inahu…”