Aminiya:
2025-02-23@22:07:14 GMT

Arewa na buƙatar haɗa kai da Kudu Maso Kudu don ceto Najeriya — El-Rufai

Published: 23rd, February 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya buƙaci manyan ‘yan siyasa daga yankin Arewa da Kudu Maso Kudu su haɗa kai gabanin zaɓen 2027.

El-Rufai, ya yi wannan kira ne yayin da ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayi dattijo kuma jagoran yankin Neja Delta, Edwin Clark.

Babu ɗan Arewa mai hankali da zai yi tallan APC a 2027 – Jigo a PDP Fasinjoji 4 sun rasu yayin da bas ta kama da wuta a Jigawa

A cewarsa, Najeriya tana cikin matsala mai tsanani kuma tana buƙatar ɗauki cikin gaggawa.

“A shekarun baya, Arewa da Kudu Maso Kudu sun kasance abokan siyasa,” in ji El-Rufai.

“Kada mu manta da hakan. Mu koma kam wannan haɗin kai. Mu ceci wannan ƙasa domin tana buƙatar ceton gaggawa. Dole ne mu ɗauki matakin ceton ƙasar nan.”

Maganganunsa sun zo ne yayin da ake raɗe-raɗin cewa yana shirin sauya sheƙa daga jam’iyyar APC.

A makonnin da suka gabata, ya gana da ’yan siyasa daga jam’iyyun adawa bayan wani saɓani tsakaninsa da jam’iyyar APC mai mulki da kuma gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

El-Rufai, wanda ya je ziyarar ta’aziyyar tare da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya yaba da rawar da Atiku ya taka wajen kawo sauye-sauyen tattalin arziƙi a lokacin mulkin Shugaba Olusegun Obasanjo.

Segun Showunmi, tsohon mai magana da yawun yaƙin neman zaɓen Atiku, ya tabbatar da cewa wannan ganawar tana cikin shirye-shiryen siyasa gabanin zaɓen 2027.

A watan Janairu, El-Rufai ya gana da Hamza Al-Mustapha, tsohon hadimin marigayi Janar Sani Abacha, da Shehu Gabam, shugaban jam’iyyar SDP, da wasu ’yan siyasa a Abuja.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa Edwin Clark Haɗin Kai rasuwa Siyasa ta aziyya

এছাড়াও পড়ুন:

Manchester United Za Ta Rage Ma’aikata

Wasu rahotannin na cewar Ratcliffe ya zuba kudin da ya kai fam miliyan (£300m) a United, domin bunkasa filin atisaye na Carringhton da tsara yadda za a fuskanci gina sabon filin wasa sannan ana jiran Ratcliffe ya bayar da izinin fara shirin gina sabon filin da za a kashe sama da fam biliyan biyu (£2bn), ko kuma a yi wa tsohon filin wasa na Old Trafford kwaskwarima da zai ci Fam biliyan 1.5.

Manchester United ta sanar da yin hasarar kasuwanci da ya kai Fam miliyan 113.2 daga ranar 30 ga watan Yunin 2024 kuma kawo yanzu kungiyar tana mataki na 15 a teburin Premier League, bayan wasan mako na 24. Amma kuma har yanzu kungiyar tana buga gasar cin kofin Europa Leage da gasar cin kofin kalubale na FA Cup da kungiyar za ta fafata da Fulham a farkon watan gobe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Har yanzu Najeriya na buƙatar shugabanni nagari – Sheikh Gumi
  • Babu ɗan Arewa mai hankali da zai yi tallan APC a 2027 – Jigo a PDP
  • Fasinjoji 4 sun rasu yayin da bas ta kama da wuta a Jigawa
  • Manchester United Za Ta Rage Ma’aikata
  • Gawuna ne ya lashe zaɓen Gwamnan Kano a 2023 — Ata
  • Hamas Ta Mika Fursinonin HKI 6 Sannan Tana Dakon A Shiga Marhala Ta Biyu
  • Babu Wani Abin Burgewa A APC, Za Mu Kori Wannan Gwamnati A 2027 – Tambuwal
  • Malamai Suna Takara Da ’Yan Siyasa Wajen Neman Mulki –Sule Lamido
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ba Za Mu Sauke Farashin Burodi Ba —’Yan kasuwa