Lebanon: An Rufe Shahid Sayyid Hassan Nasrallah A Makwancinsa Na Karshe A Birnin Beirut
Published: 23rd, February 2025 GMT
Lokacin kadan da ya gabata ne dai aka rufe shahid Sayyid Hassan Nasrallah a makwancinsa na kare dake kusa da filin saukar jiragen sama na Beirut,bayan da aka dauki tsawon yau ana gudanar da jana’izarsa.
Dubun dubatar mutanen Lebanon da kuma wasu daga wajen kasar ne su ka halarci taron jana’izar Sayyid Shahid Hassan Nasrallah da kuma ta Sayyid Hashim Safiyuddin da aka gudanar a cikin birnin Beirtu.
Tashar talabijin din al’mayadin ta bayyana cewa bisa kirdado adadin mutanen da su ka halarci jana’izar sun kai mutane miliyan daya da 400,000.
Mahalarta jana’izar sun cika filin wasa na birnin Beirut da kuma manyan tituna ta yadda babu masaka cinke, da hakan ya sa motar da take dauke da makararsa da kuma ta Sayyid Hashim Safiyuddin ta rike tafiya a cikin nawa.
An fara gudanar da taron jana’izar ne dai da takaitattun jawabai daga wakilin jagoran juyin musulunci na Iran da kuma na babban sakataren kungiyar ta Hizbullah Sheikh Na’im Kassim.
A tsawon lokacin da motar dake dauke da makarar Sayyid Shahid take tafiya an rika watsa jawaban Shahidin da ya yi a lokuta mabanbanta a tsawon rayuwarsa da suke da alaka da yin jinjina ga al’ummar Lebanon,musamman masu bai wa gwgawarmaya kariya da goyon baya.
Lokaci kadan da ya gabata ne dai aka shigar da makarar da take da Sayyid Hassan Nasarallah cikin makwancinsa na karshe, a daidai lokacin da ake karanta suratu Yasin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’an Diblomasiyya Daga Kungiyar G20 Da Dama Sun Isa Afrika Ta Kudu
Jami’an diblomasiyya da dama daga kasashen kungiyar G20 ne suka isa birnin Johannesburg na kasar Afirka ta kudu, don halattar taro na kwanaki biyu.
Ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Lavrov ya isa birnin Johannesburg a jiya Alhamis kwanaki biyu kacal da ya gana da tokwaransa na kasar Amurka a birnin Riyad na kasar Saudiya.
Shafin yanar gizo na labarai ‘Africa News’ yace ana saran kasashen turai zasu kara jaddada goyon bayansu ga kasar Ukraine a yakin da take fafatawa da kasar Rasha. Duk tare da cewa gwamnatin kasar Amurka tana son kawo karshen yakin ba tare da su ba.
Kasashen Burtaniya , Faransa, Jamus da kuma tarayyar Turai EU gaba daya suna goyon bayan Ukraine a yakinta da Rasha.
Har’ila yau sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio bai bayyana a taron ba. Sai dai ana zaton jakadan kasar Amurka a kasar Afirka ta kudu Dana Brown ne zata wakilci kasar a taron.
Amurka ta ki halattar taron G20 A Afrika ta Kudu ne saboda matsayinta dangane da yaki a Gaza da kuma wasu dokokin mallaka a kasarsa.