Birtaniya Da Faransa suna Son Aikewa Da Sojojin Turai 30,000 Kasar Ukiraniya
Published: 23rd, February 2025 GMT
Jaridar Wall Satreet Journal ta ambaci cewa kasashen Faransa da Birtaniya suna shirya yiyuwar aikewa da sojojin tabbatar da zaman lafiya a cikin kasar Ukiraniya idan an tsagaita wutar yaki.
Jaridar ta Amurka ta kuma kara da cewa; Idan an kai ga cimma tsagaita wutar yaki to da akwai yiyuwar turawan za su aike da sojojin zaman lafiya da za su kai 30,000 daga cikin har da na kasar Switzerland.
Sai dai kuma aiwatar da shirin na turai yana da alaka ne da yadda Donald Trump zai amince da kasarsa ta taka rawa, idan har Rasha ta kai wa turawan hari, ko ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta, kamar yadda jaridar ta ambato wani jami’in turai din yana fada.
Jaridar ta kara da cewa turawan ba za su bukaci Amukan ta aike da sojoji tare da su zuwa Ukiraniya din ba, sai dai za su bukaci taimakonta da kayan aikin da ba su da su.
A ranar Alhamis mai zuwa ne ake sa ran cewa Fira ministan Birtaniya Sir Keir Rodney Starmer zai tattauna shirin nasu na turai da shugaban kasar Amurka Donald Trump.
A gefe daya, kwamandan sojojin kasar Switzerland Laftanar Janar Thomas Sussli ya bayyana cewa, kasarsa za ta iya taimakawa da wani adadi na sojojin zaman lafiya anan gaba,idan har gwamnatin Ukiraniyan ta bukaci hakan.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gobara ta ƙone gidaje, amfanin gona da dabbobi a Borno
Wata gobara ta tashi a ƙauyen Bukar da ke Ƙaramar Hukumar Konduga a Jihar Borno, ta yi ɓarna mai tarin yawa.
Gobarar ta lalata gidaje, amfanin gona, da dabbobi na miliyoyin Naira, amma babu wanda ya rasa ransa.
’Yan bindiga sun harbe fasto, sun sace wasu a coci Gawuna ne ya lashe zaɓen Gwamnan Kano a 2023 — AtaWani mazaunin ƙauyen ya ce gobarar ta fara ne daga wutar girki a wani gida, sai iska mai ƙarfi ta bazata zuwa wasu gidaje, lamarin da ya sa mutane suka kasa shawo kanta.
Bayan kamawar wutar, sojojin Najeriya da ke yankin sun garzaya domin kai ɗauki.
Sun taimaka wajen kashe wutar tare da ceton tsofaffi da yara.
Kazalika, gobarar ta cinye wani ɓangare na kasuwar ƙauyen, inda ta ƙone shaguna da rumfunan abinci.
Mazauna ƙauyen sun ce yanayin iskar da ake yi a lokacin ya ƙara ta’azzara gobarar, hakan ya sa aka wahala wajen kashe ta.
Duk da hatsarin da ke tattare da wutar, sojoji sun taimaka wajen daƙile gobarar, wanda ya hana ta bazuwa zuwa wasu wurare, ciki har da makarantar ƙauyen.
Shugabannin yankin sun nuna godiyarsu ga sojojin da suka kawo musu ɗauki cikin gaggawa.
“Ba don taimakon Allah da na sojoji ba, gobarar na iya haddasa asarar rayuka,” in ji wani mazaunin ƙauyen, Bukar Usman.
A halin yanzu, Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno (SEMA), ta tura tawaga domin tantance asaea tare da raba kayan agaji ga waɗanda gobarar ta shafa.