Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin ya yi Allah wadai da kasar Australia bisa yadda ta zargi kasar Sin da yin atisayen soja bisa doka a tekun dake kusa da kasar ta Australia.

Kakakin, Wu Qian ya bayyana hakan yayin da yake amsa tambayoyin kafofin watsa labaru game da zargin na Australia cewa jiragen ruwan yaki uku na kasar Sin sun yi atisayen soja a tekun dake kusa da kasar Australia.

Wu Qian ya bayyana cewa, zargin da kasar Australia ta yi ba shi da tushe balle makama, domin yankin tekun da jiragen ruwan yakin na kasar Sin suka yi atisayen soja yana can nesa da layin teku na kasar Australia, kuma yanki ne da ba ya cikin mallakar wata kasa. Kakakin ya kara da cewa, kafin lokacin, sai da kasar Sin ta ba da sanarwa sau da dama a kan gudanar da atisayen, sai dai kuma abin mamaki, bayan da jiragen ruwan yakin kasar suka harba boma-bomai zuwa tekun, sai Australiya ta yi zargin.

Ya ce, Sin ta gudanar da ayyukan atisayen bisa dokokin kasa da kasa da ka’idojin zirga-zirga na kasa da kasa, wadanda ba za su kawo illa ga tsaron zirga-zirgar jiragen sama ba. Kuma kasar ta Australia ta san lamarin, amma kuma ta zargi kasar Sin da abin da ba shi da tushe balle makama, kuma Sin tana nuna rashin jin dadinta game da batun. (Zainab Zhang)

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Australia

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Luguden Wuta Kan Gabar Yammacin Kogin Jordan

Fira ministan gwamnatin mamayar Isra’ila ya ba da umarnin tsananta kai hare-hare kan yankunan yammacin gabar kogin Jordan biyo bayan hare-haren bama-bamai da aka kai a birnin Tel Aviv

Fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu ya bada umarnin kai hare-haren wuce gona da iri kan sansanin ‘yan gudun hijira na Tulkaram da ke arewacin gabar yammacin kogin Jordan a jiya Juma’a.

Yanzu kusan wata guda ke nan da Netanyahu ya ba da umarnin tsananta hare-haren kan sansanin ‘yan gudun hijiran na Tulkram, kamar yadda ofishinsa ya bayyana, kwana guda bayan tashin bama-bamai kan motocin bus-bus a yankin Bat Yam da ke kudancin birnin Tel Aviv fadar mulkin haramtacciyar kasar Isra’ila.

Ofishin fira ministan ya bayyana cewa: Kwanan nan ne Netanyahu ya ziyarci sansanin ‘yan gudun hijira na Tulkaram” inda ya ba da umarnin kara kai hare-haren wuce gona da iri kan yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Birtaniya Da Faransa suna Son  Aikewa Da Sojojin Turai 30,000 Kasar Ukiraniya
  • Sojojin Ruwa Da Kuma Sojijin Sama Na JMI Sun Hada Guiwa Don Yin atisaye Tare Mai taken Zulfikar
  • Yake-Yaken Kasa Da Kasa Ne Suka Mamaye Taron G20 Na Ministocin Harkokin Wajen Kungiyar A Afirka Ta Kudu
  • Kungiyar Hizbullah Ta Lebanon Ta Jaddada Rashin Amincewarta Da Mika Kan Kasar Ga Amurka Da Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Sojojin Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Luguden Wuta Kan Gabar Yammacin Kogin Jordan
  • Sojojin Faransa Sun Mika Sansanin Soji Mafi Girma Da Suka Mamaye Ga Sojojin Faransa
  • Jirgin Saman Da Kasar Sin Ta Kera Mai Amfani Da Lantarki Ya Yi Tashin Farko Cikin Nasara
  • Tashar Jiragen Sama Ta Rafikul Hariri Int. Na Birnin Beirut Yana Ciki Da Masu Shiga Kasar Saboda Jana’izar Shaheed Nasarallah
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Suke Da Hakkin Yanke Shawarar Makomar Kaarsu Ba Amurka Ba