Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ya Yi Fatali Da Zargin Australia A Kan Atisayen Sojojin Kasar
Published: 23rd, February 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin ya yi Allah wadai da kasar Australia bisa yadda ta zargi kasar Sin da yin atisayen soja bisa doka a tekun dake kusa da kasar ta Australia.
Kakakin, Wu Qian ya bayyana hakan yayin da yake amsa tambayoyin kafofin watsa labaru game da zargin na Australia cewa jiragen ruwan yaki uku na kasar Sin sun yi atisayen soja a tekun dake kusa da kasar Australia.
Wu Qian ya bayyana cewa, zargin da kasar Australia ta yi ba shi da tushe balle makama, domin yankin tekun da jiragen ruwan yakin na kasar Sin suka yi atisayen soja yana can nesa da layin teku na kasar Australia, kuma yanki ne da ba ya cikin mallakar wata kasa. Kakakin ya kara da cewa, kafin lokacin, sai da kasar Sin ta ba da sanarwa sau da dama a kan gudanar da atisayen, sai dai kuma abin mamaki, bayan da jiragen ruwan yakin kasar suka harba boma-bomai zuwa tekun, sai Australiya ta yi zargin.
Ya ce, Sin ta gudanar da ayyukan atisayen bisa dokokin kasa da kasa da ka’idojin zirga-zirga na kasa da kasa, wadanda ba za su kawo illa ga tsaron zirga-zirgar jiragen sama ba. Kuma kasar ta Australia ta san lamarin, amma kuma ta zargi kasar Sin da abin da ba shi da tushe balle makama, kuma Sin tana nuna rashin jin dadinta game da batun. (Zainab Zhang)
কীওয়ার্ড: kasar Australia
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Taron Tattaunawar Kasa Da Kasa Kan Damammakin Da Sin Ke Gabatarwa A Rasha
Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin, wato CMG ya gabatar da taron tattaunawar kasa da kasa mai taken “Sin a lokacin bazara: More damammakin da take gabatarwa ga duniya” a ran 20 ga watan nan da muke ciki a kasar Rasha. Kuma Shugaban CMG Shen Haixiong ya gabatar da jawabi ta kafar bidiyo.
Jakadan Sin dake kasar Rasha, Zhang Hanhui da wakilan bangaren siyasa da ba da ilmi da yada labarai na kasar Rasha sun halarci taron don tattaunawa kan hadin gwiwar tattalin arzikin kasashen biyu da kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da musanyar al’adu da kuma hadin kan kafofin yada labarai da sauransu. Wakilai na Rasha sun hada da Andrey Denisov, mataimakin shugaba na farko na kwamiti mai kula da harkokin ketare na tarayyar kasar Rasha, da kuma Alexander Yakovenko, mataimakin babban manajan rukunin yada labarai na“Rossiya Segodnya”,kana da Andrey Margolin, mataimakin shugaban kwalejin nazarin tattalin arziki da harkokin al’umma dake karkashin shugaban Rasha wato (RANEPA), da Yuri Mazei, mataimakin shugaban jami’ar Lomonosov Moscow, kana da Mikhail Chkanikov, babban editan jaridar “Arguments and Facts”. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp