Aminiya:
2025-03-26@06:33:35 GMT

Har yanzu Najeriya na buƙatar shugabanni nagari – Sheikh Gumi

Published: 24th, February 2025 GMT

Fitaccen Malamin Addinin Musuluncin nan, Sheikh Ahmad Gumi, ya ce har yanzu Najeriya na neman shugabanni nagari da za su fifita jin daɗin al’umma maimakon mayar da hankali kan wajen tara wa kansu dukiya.

Ya bayyana hakan ne yayin bikin karramawa da ƙungiyar tsofaffin ɗaliban Makarantar Firamare ta Sultan Bello (SUBOPA), ta shirya domin girmama wasu mambobinta biyu – Manjo Janar Abdulmalik Jibrin (mai ritaya) da Birgediya Janar Abdulkadir Gumi (mai ritaya), bisa sababbin muƙaman da suka samu a gwamnati.

Arewa na buƙatar haɗa kai da Kudu Maso Kudu don ceto Najeriya — El-Rufai Babu ɗan Arewa mai hankali da zai yi tallan APC a 2027 – Jigo a PDP

An naɗa Manjo Janar Jibrin a matsayin Sakatare na Hukumar Kula da Tsaro na Fararen Hula, yayin da aka naɗa Birgediya Janar Gumi a matsayin Shugaban Kwamitin Tallafin Tsaro na Jihar Zamfara.

Sheikh Gumi ya yaba wa Manjo Janar Jibrin bisa aiki tuƙuru da ɗa’a, inda ya ce har yanzu Najeriya na buƙatar shugabanni kamar shi waɗanda ke da gaskiya, horo mai kyau, da kuma kishin al’umma.

“Wannan ya faru ne saboda Najeriya na matuƙar buƙatar shugabanni nagari da za su jagoranci ƙasar nan.

“Muna buƙatar mutane masu tarbiyya da ladabi waɗanda ke da niyyar taimaka wa wasu, ba kawai kansu ba.

“Mutanen da ke da kyawawan halaye da ɗabi’u su ne ya kamata ake bai wa muƙaman shugabanci a ƙasar nan,” in ji shi.

Ya kuma soki shugabannin yanzu, inda ya ce: “Ba irin shugabannin da muke da yanzu a ƙasar nan ba, waɗanda kawai ke tunanin kansu da iyalansu.”

Da yake magana kan matsalolin da Najeriya ke fuskanta, Sheikh Gumi ya nuna damuwarsa kan tasirin matsalar tsaro, musamman a jihohin da suka haɗa da Zamfara, inda matsalar ta janyo koma baya a ɓangaren ilimi tare da haifar da rashin zaman lafiya a wasu yankuna.

Ya jinjina wa Gwamnatin Jihar Zamfara bisa bai wa Birgediya Janar Gumi muƙami, wanda ya ce zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro.

A nasa jawabin, Shugaban SUBOPA, Mohammad Babayo Hassan, ya ce naɗin da aka yi wa mambobinsu ba kawai nasararsu ba ce, wata alama ce ta ɗabi’u da ƙwazon da suka koya daga makarantarsu.

Da yake magana a madadin waɗanda aka karrama, Manjo Janar Abdulmalik Jibrin ya keɓe lambar yabon ba ta shi ce shi kaɗai ba, face ta dukkan mambobin ƙungiyar ne.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya Najeriya na Manjo Janar na buƙatar

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Kafa Rundunar Daukin Gaggawa Don Magance Matsalolin Tsaro

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta kafa runduna ta musamman a kasar don magance matsalolin tsaro daban-daban wadanda kasar take fama das u.

Jaridar Premium times ta Najeriya ta nakalto ministan tsaron kasar Muhammad Badaru yana fadar haka a lokacinda yake kaddar da wani bangaren na rundunar a barikin Kabala da ke barikin Jaje a kusa da birnin Kaduna daga arewacin kasar a jiya Litinin.

Badaru ya kara da cewa gwamnatin kasar tag a akwai butara da samar da irin wannan rundunar, saboda magance matsalolin tsaro daban-daban wadanda aka dade ana fama das u, ko kuma wadanda suke tasowa nan da ca.

Ya kara da cewa rundunar da aka kaddamar a jiya litinin bangare ne na runduna mai sojoji 800 da za’a samar saboda wannan gagarumin aikin tabbatar da tsaro a kasar. Idan an kammala hurasda sojojin zasu zama abin dogaro a lokacinda ake bukatar daukin gaggawa a ko ina a kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araqchi: Har yanzu Iran ba ta mayar da amsa ga wasikar Trump kan tattaunawar nukiliya ba
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Kafa Rundunar Daukin Gaggawa Don Magance Matsalolin Tsaro
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Ƙasa Kiranye
  • Fursunoni 12 sun tsere bayan fasa gidan yari a Kogi
  • NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci
  • Yadda garin Zip ya nutse a Kogin Binuwai