Har yanzu Najeriya na buƙatar shugabanni nagari – Sheikh Gumi
Published: 24th, February 2025 GMT
Fitaccen Malamin Addinin Musuluncin nan, Sheikh Ahmad Gumi, ya ce har yanzu Najeriya na neman shugabanni nagari da za su fifita jin daɗin al’umma maimakon mayar da hankali kan wajen tara wa kansu dukiya.
Ya bayyana hakan ne yayin bikin karramawa da ƙungiyar tsofaffin ɗaliban Makarantar Firamare ta Sultan Bello (SUBOPA), ta shirya domin girmama wasu mambobinta biyu – Manjo Janar Abdulmalik Jibrin (mai ritaya) da Birgediya Janar Abdulkadir Gumi (mai ritaya), bisa sababbin muƙaman da suka samu a gwamnati.
An naɗa Manjo Janar Jibrin a matsayin Sakatare na Hukumar Kula da Tsaro na Fararen Hula, yayin da aka naɗa Birgediya Janar Gumi a matsayin Shugaban Kwamitin Tallafin Tsaro na Jihar Zamfara.
Sheikh Gumi ya yaba wa Manjo Janar Jibrin bisa aiki tuƙuru da ɗa’a, inda ya ce har yanzu Najeriya na buƙatar shugabanni kamar shi waɗanda ke da gaskiya, horo mai kyau, da kuma kishin al’umma.
“Wannan ya faru ne saboda Najeriya na matuƙar buƙatar shugabanni nagari da za su jagoranci ƙasar nan.
“Muna buƙatar mutane masu tarbiyya da ladabi waɗanda ke da niyyar taimaka wa wasu, ba kawai kansu ba.
“Mutanen da ke da kyawawan halaye da ɗabi’u su ne ya kamata ake bai wa muƙaman shugabanci a ƙasar nan,” in ji shi.
Ya kuma soki shugabannin yanzu, inda ya ce: “Ba irin shugabannin da muke da yanzu a ƙasar nan ba, waɗanda kawai ke tunanin kansu da iyalansu.”
Da yake magana kan matsalolin da Najeriya ke fuskanta, Sheikh Gumi ya nuna damuwarsa kan tasirin matsalar tsaro, musamman a jihohin da suka haɗa da Zamfara, inda matsalar ta janyo koma baya a ɓangaren ilimi tare da haifar da rashin zaman lafiya a wasu yankuna.
Ya jinjina wa Gwamnatin Jihar Zamfara bisa bai wa Birgediya Janar Gumi muƙami, wanda ya ce zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro.
A nasa jawabin, Shugaban SUBOPA, Mohammad Babayo Hassan, ya ce naɗin da aka yi wa mambobinsu ba kawai nasararsu ba ce, wata alama ce ta ɗabi’u da ƙwazon da suka koya daga makarantarsu.
Da yake magana a madadin waɗanda aka karrama, Manjo Janar Abdulmalik Jibrin ya keɓe lambar yabon ba ta shi ce shi kaɗai ba, face ta dukkan mambobin ƙungiyar ne.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya Najeriya na Manjo Janar na buƙatar
এছাড়াও পড়ুন:
Sheikh Kassim: Gwagwarmaya Za Ta Ci Gaba Da Dukkanin Karfinta
Babban sakataren kungiyar Hizbullah Sayyid Hassan Nasrallah Sheikh Na’im Kassim ya bayyana Shahidin al’umma Sayyid Hassan Nasrallah da cewa, jagora ne na musamman na al’ummun larabawa da musulmi kuma shugaban gwgawarmaya.
A cikin jawabin da ya gabatar a lokacin jana’izar Shahid Sayyid Hassan Nasrallah, da Shahid Hashim Safiyuddin, inda ya bayyan cewa: A wannan rana muna yin ban kwana da jagora na tarihi na musamman wanda kuma yake a matsayin alkiblar ‘yantattun na duniya. Sheik Na’im Kassim ya kuma ce; Sayyid Hassan Nasrallah ya kasance wanda ‘yan gwgawarmaya suke kauna, wanda Falasdinu da birnin Kudus ne manufarsa, ya kuma taka rawa wajen farfado da batun kare hakkokin Falasdinawa.
Babban sakataren kungiyar ta Hizbullah Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce; Sayyid Shahid Hassan Nasrallah ya narke a cikin yi wa musulunci hidima da kuma a cikin riko da wilaya, ya kuwa yi shahada ne a sahun gaba na fagen daga, kuma zai ci gaba da zama a cikin zukatanmu da ruhinmu, za kuma mu yi riko da amana mu ci gaba da tafiya akan wannan tafarkin.
Shekih Na’im Kassim wanda ya yi Magana da sayyid Nasrallah, ya ce: Kai ne kake fadin cewa, tare za mu kammala wannan tafiyar,ko da kuwa za a kashe mu baki daya. Ya Sayyid Nasrallah muna nan akan wannan alkawalin.”
Sheikh Kassim ya kuma ce; Taron da aka yin a jana’iza, yana a matsayin bayyana ra’ayi ne akan riko da gwagwarmaya wanda irinsa ya yi karanci a tarihin Lebanon.