Gwamnatin Tarayya ta yi kira ga ‘yan Najeriya da su rika ba da muhimman bayanai ga hukumomin tsaron  kasar nan.

Ministan tsaro, Alhaji Badaru Abubakar ne ya yi wannan kiran a lokacin da yake jawabi a wani taron jama’a na gwamnatin jihar Jigawa da aka gudanar a karamar hukumar Birnin Kudu.

A cewar sa, kiran ya zama wajibi domin karfafa tsaro a fadin Najeriya.

Alhaji Badaru Abubakar, ya yi nuni da cewa an samu ingantuwar harkokin tsaro a fadin kasar cikin ‘yan watannin nan.

Ya kuma bayyana cewa, gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta yi iya bakin kokarinta wajen yaki da rashin tsaro, kuma za ta ci gaba da jajircewa wajen cimma manufofin da ake so.

Ministan ya yi nuni da cewa, gwamnatin tarayya za ta ci gaba da bayar da duk wani tallafi ga sojojin Najeriya da ke fagen fama don tabbatar da an maido da tsaro.

Badaru Abubakar wanda shi ne tsohon gwamnan jihar Jigawa, ya bayyana jin dadinsa da yadda ya mika ragamar shugabanci ga gwamnati mai inganci.

Ya yabawa gwamnatin Gwamna Umar Namadi bisa gagarumin ayyukan raya kasa da aka gudanar a jihar cikin shekara daya da rabi.

“Na yi farin cikin ganin manyan  ayyukan raya kasa da wannan gwamnati ta aiwatar, a cikin shekara daya da rabi da ta wuce,” in ji Ministan.

Gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, wasu daga cikin manyan baki da suka halarci bikin sun hada da, mataimakin gwamnan jihar, Injiniya Aminu Usman, da tsohon gwamnan jihar  Barista Ali Sa’ad Birnin Kudu, da sakataren gwamnatin jihar Malam Bala Ibrahim, da sarakuna da malaman addinai, da manyan jami’an gwamnati da dai sauransu.

 

Usman Muhammad Zaria.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Ministan Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Bukaci Hanzarta Hukunta Shugabannin ‘Yan Sahayoniyya Kan Laifukan Da Suka Aikata

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya yi kira da a gaggauta bibiyar bayanan manyan laifuka na shugabannin gwamnatin mamayar Isra’ila

A wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na kasar Holland, ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya yi Allah wadai da ci gaba da mamaya da kuma laifukan da yahudawan sahayoniyya suke yi a Falasdinu, tare da yin kira ga kasashen duniya da su dauki matakin gaggawa wajen hanzarta bibiyar bayanan shari’a da laifuka a kotunan duniya dangane da kisan kiyashi da laifukan yaki da shugabannin mamayar Isra’ila suka aikata.

Kamfanin dillancin labaran Fars ya habarta cewa: Ministan harkokin wajen kasar Holand Caspar Veldkamp da takwaransa na Iran Abbas Araqchi sun tattauna kan batutuwan da suka shafi kasashen biyu da ci gaban kasa da kasa a wata tattaunawa ta hanyar wayar tarho a jiya Asabar.

Haka nan kuma yayin da yake ishara da dogon tarihin dangantakar da ke tsakanin Iran da Netherlands, ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye ta ke ta gudanar da dukkanin harkokin da suka shafi kasashen biyu bisa mutunta juna da moriyarsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Katsina Ta Kashe Naira Biliyan 5.7 Wajen Sayen Awaki 40,000 Domin Raba Wa Mata
  • Iran Ta Bukaci Hanzarta Hukunta Shugabannin ‘Yan Sahayoniyya Kan Laifukan Da Suka Aikata
  • PDP ta lashe zaɓen ƙananan hukumomin Osun
  • Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kano ta raba kayan tallafi
  • Sojojin Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Luguden Wuta Kan Gabar Yammacin Kogin Jordan
  • Dalilan ƙara kuɗin Jami’ar Gombe — Gwamna Inuwa
  • Gwamnatin Yobe za ta gina gadar sama a kan N22.3bn
  • Gwamnatin Filato ta dakatar da haƙar ma’adinai saboda matsalar tsaro
  • UNICEF Ya Jinjinawa Jihar Jigawa