Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Al’umma Da Su Rika Taimakawa Hukumomin Tsaro Da Muhimman Bayanai
Published: 24th, February 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta yi kira ga ‘yan Najeriya da su rika ba da muhimman bayanai ga hukumomin tsaron kasar nan.
Ministan tsaro, Alhaji Badaru Abubakar ne ya yi wannan kiran a lokacin da yake jawabi a wani taron jama’a na gwamnatin jihar Jigawa da aka gudanar a karamar hukumar Birnin Kudu.
A cewar sa, kiran ya zama wajibi domin karfafa tsaro a fadin Najeriya.
Alhaji Badaru Abubakar, ya yi nuni da cewa an samu ingantuwar harkokin tsaro a fadin kasar cikin ‘yan watannin nan.
Ya kuma bayyana cewa, gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta yi iya bakin kokarinta wajen yaki da rashin tsaro, kuma za ta ci gaba da jajircewa wajen cimma manufofin da ake so.
Ministan ya yi nuni da cewa, gwamnatin tarayya za ta ci gaba da bayar da duk wani tallafi ga sojojin Najeriya da ke fagen fama don tabbatar da an maido da tsaro.
Badaru Abubakar wanda shi ne tsohon gwamnan jihar Jigawa, ya bayyana jin dadinsa da yadda ya mika ragamar shugabanci ga gwamnati mai inganci.
Ya yabawa gwamnatin Gwamna Umar Namadi bisa gagarumin ayyukan raya kasa da aka gudanar a jihar cikin shekara daya da rabi.
“Na yi farin cikin ganin manyan ayyukan raya kasa da wannan gwamnati ta aiwatar, a cikin shekara daya da rabi da ta wuce,” in ji Ministan.
Gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, wasu daga cikin manyan baki da suka halarci bikin sun hada da, mataimakin gwamnan jihar, Injiniya Aminu Usman, da tsohon gwamnan jihar Barista Ali Sa’ad Birnin Kudu, da sakataren gwamnatin jihar Malam Bala Ibrahim, da sarakuna da malaman addinai, da manyan jami’an gwamnati da dai sauransu.
Usman Muhammad Zaria.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Ministan Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
Gwamnatin jihar Jigawa ta bada kwangilar sanya kwalta akan hanyar Dolen kwana zuwa Garin Gabas zuwa Hadejia, kan naira miliyan dubu bakwai da miliyan dari takwas.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan a wajen bikin kaddamar da aikin sanya kwaltar.
Ya ce aikin hanyar mai tsawon kilomita 29, ana sa ran kammalawa nan da watanni 12 masu zuwa.
Malam Umar Namadi ya kara da cewar, an bada aikin sanya kwaltar ne da kuma sauran ayyukan inganta hanyoyi domin saukakawa manoma da sauran al’umma harkokin sufuri.
A don haka, ya yi kira ga al’ummar jihar da su rinka sa ido akan kayayyakin da hukuma ta samar musu domin gudun lalacewa da kuma barnatarwa.
A jawabinsa na maraba, kwamishinan ayyuka na Jihar, Injiniya Gambo S Malam ya ce gwamnatin jihar, ta bada ayyukan hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, bikin ya samu halartar Ministar ma’aikatar Ilmi Dr. Suwaiba Ahmed Babura da Sanata Ahmed Abdulhamid Malam Madori da kakakin majalissar dokokin jihar Alhaji Haruna Aliyu Dangyatum da manyan jami’an gwamnatin jihar.
Usman Mohammed Zaria