Aminiya:
2025-03-26@21:59:50 GMT

NAJERIYA A YAU: Matakan Kariya Daga Cutar Ƙyandar Biri

Published: 24th, February 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Cutar ƙyandar biri da aka fi sani da Mpox ta ƙara ɓulla a Najeriya.

Na baya-bayan nan shi ne ɓullarta a Jihar Filato inda aka samu mutum 11 da suka kamu da ita, sai wanda ya rasa ransa mutum ɗaya.

Cutar ta ɓulla ne a ƙananan hukumomi biyar da suka haɗa da Jos ta Arewa da Bokkos da Shendam da Mangu da kuma Kenke.

Ko waɗanne irin matakai ya kamata al’umma su ɗauka don kauce wa kamuwa da wannan cuta?

NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ba Za Mu Sauke Farashin Burodi Ba —’Yan kasuwa DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Najeriya Ke Haɗa Buga-Buga Da Aikin Albashi

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan matakan kariya daga cutar ƙyandar biri.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Annobar kyandar Biri cutar ƙyandar biri kariya ƙyandar biri matakan kariya matakan kariya daga cutar ƙyandar biri

এছাড়াও পড়ুন:

NIDCOM: An Ceto ‘Yan Nijeriya Sama Da 950 Daga Gidajen Kurkuku A Libya

Hukumar kula da ‘yan Nijeriya mazauna ƙasashen ƙetare (NIDCOM), ta bayyana cewa an kuɓutar da ‘yan Nijeriya 956 daga gidajen yarin Libya tare da mayar da su gida cikin watanni ukun farkon shekarar 2025.

Shugabar hukumar, Hon. Abike Dabiri-Erewa, ta ce waɗanda aka dawo da su sun haɗa da mata 683, maza 132, yara 87, da jarirai 54.

An samu nasarar mayar da su ne sakamakon haɗin gwiwa tsakanin NIDCOM, Hukumar ‘Yan Gudun Hijira ta Duniya (IOM) da kuma Hukumar Kula da Baƙin Haure da waɗanda rikici ya raba da matsugunansu (NCRMI).

A cewar sanarwar da NIDCOM ta fitar, an dawo da su ne kashi-kashi daga watan Janairu zuwa Maris 2025.

A ranar 28 ga Janairu, an dawo da mutum 152. A ranakun 11, 19, da 25 ga Fabrairu, an dawo da mutum 484. A ranakun 4 da 18 ga Maris, an dawo da mutum 320.

Dabiri-Erewa ta ƙara da kira ga ‘yan Nijeriya da su guji tafiya ƙetare ta ɓarauniyar hanya, musamman ta Libya, wacce ke fama da matsaloli da rikici.

Ta kuma jaddada cewa wajibi ne ‘yan Nijeriya su bi hanyoyin da doka ta tanada idan suna son yin hijira, domin guje wa hatsarin da ke tattare da tafiya ta haramtacciyar hanya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 2 sun rasu, wani ya ji rauni a hatsarin mota a Kano
  • Kwalara Ta Kashe Mutum 14, Ana Zargin 886 Sun Kamu A Nijeriya – NCDC
  • NIDCOM: An Ceto ‘Yan Nijeriya Sama Da 950 Daga Gidajen Kurkuku A Libya
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18]
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Kafa Rundunar Daukin Gaggawa Don Magance Matsalolin Tsaro
  • Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi
  • Mutum 2,000 za su riƙa kamuwa da cutar HIV duk rana a duniya — MDD
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Ƙasa Kiranye
  • Sin Ta Sanar Da Dokar Dakile Takunkuman Kasashen Waje
  • NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci