HausaTv:
2025-02-24@09:34:41 GMT

Hamas ta yaba da irin goyon bayan da Sayyed Nasrallah ya baiwa Falasdinu

Published: 24th, February 2025 GMT

Kungiyar Hamas ta jinjina da irin babbar gudunmawa da tsayin dakan da Sayyed Hassan Nasrallah da Sayyed Hashem Safieddine suka yi wajen goyon bayan Palastinu, da kuma shahadar da suka yi a kan wannan tafarki.

A cikin wata sanarwa da ta fitar dangane da jana’izar shahidan biyu, kungiyar Hamas ta ce, muna addu’ar Allah ya jikan su da rahama, tare da mika ta’aziyyarmu ga al’ummar kasar Labanon da dukkanin al’ummar mu Larabawa da musulmi.

Kungiyar ta tabbatar da cewa, laifuffukan Haramtacciyyar Kasar Isra’ila da kuma kisan gillar da ta yi wa shugabannin gwagwarmaya a Falasdinu, Labanon da sauran su, ba za su dakatar da tafarkinmu ba.

Har ila yau sanarwar ta bayyana matsayin shahid Sayyid Hassan Nasrallah da jajircewarsa da kuma sadaukar da kai ga al’ummar Palastinu, tare da yabawa kudurinsa na kafa wata hanya ta taimakawa da kuma goyon bayan al’ummar Gaza wajen tinkarar mummunan zaluncin yahudawan sahyoniyawan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wang Yi: Sin Za Ta Ci Gaba Da Mara Baya Ga Garambawul Na Kungiyar WTO 

Ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi ya bayyana a jiya Jumma’a cewa, kasar Sin tana goyon bayan tsarin ciniki cikin ‘yanci tare da zaman kungiyar ciniki ta duniya, watau WTO a matsayin wadda za ta yi uwa-ta-yi-makarbiya a kan tsarin, kuma za ta ci gaba da mara baya ga yin garambawul a kungiyar ta kasa da kasa.

Wang, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da babbar darektar WTO, Ngozi Okonjo-Iweala, a gefen taron ministocin harkokin wajen kasashen G20, a birnin Johannesburg, birni mafi girma kuma cibiyar hada-hadar tattalin arzikin Afirka ta Kudu.

A nata bangaren, Okonjo-Iweala, ta bayyana cewa, a tsakiyar rudanin da duniya ke fama da shi, kasar Sin ta hau kan turba mai kyau, da cimma burin rage talauci da MDD ta sanya a gaba tun kafin cikar wa’adin da aka sa, da bunkasa masana’antu cikin hanzari, da kuma samun nasarori a fannin ilimi, tana mai cewar, nasarar da kasar Sin ta samu ta zama abar koyi ga sauran kasashe masu tasowa.

Darektar ta kungiyar WTO ta yaba da kudurin kasar Sin na warware takaddamar ciniki ta hanyar yin shawarwari da tuntubar juna bisa tafarkin da ya hade sassa daban-daban cikin kaifin basira da nuna dattaku. Ta kuma ce, kungiyar ta WTO na fatan ci gaba da samun goyon baya mai karfi daga kasar Sin wajen inganta yin garambawul a cikinta. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lebanon: An Rufe Shahid Sayyid Hassan Nasrallah A Makwancinsa Na Karshe A Birnin Beirut
  • Sheikh Kassim: Gwagwarmaya Za Ta Ci Gaba Da Dukkanin Karfinta
  • Wakilin Jagoran Juyi A Wurin Jana’izar Sayyid: Gwgawarmaya Za Ta Ci Gaba
  • Mai Pataskum ya buɗe masallacin garin Danga a Yobe
  • Magoya Bayan Tottenham Sun Yi Zanga-Zanga
  • Wang Yi: Sin Za Ta Ci Gaba Da Mara Baya Ga Garambawul Na Kungiyar WTO 
  • Hamas, Da OIC Sun Yi Allawadai Da Dirar Mikiyan Da HKI Take Yi A Tulkaram Na Yankin Yamma Da Kogin Joirdan
  • Tawagogi Na Isa Lebanon Domin Halartar Jana’izar Sayyed Hassan Nasrallah
  • Jami’an Diblomasiyya Daga Kungiyar G20 Da Dama Sun Isa Afrika Ta Kudu