Aminiya:
2025-03-28@03:13:59 GMT

Yadda jama’a suka kama ɗan shekara 65 ɗauke da bindiga

Published: 24th, February 2025 GMT

Al’ummar gari sun wani ɗan shekara 65 dauke da bindiga sun damƙa shi a hannun hukumar ’yan sanda.

Rundunar ’yan sandan Jihar Akwai Ibom ta kama mutumin ne tare da wani abokinsa da bindiga kirar ‘Double Barrell’ da harsasai da cocila da sauran kayayyaki a cikin wata kakar matafiya.

Kakakin rundunar, DSP Timfon John, ya ce dubun dan shekara 65 din mai suna Nehemiah Sunday Udo ne a ranar Asabar baya al’ummar kauyen Ekpene Obo da ke Ƙaramar Hukumar Esit Eket sun ritsa shi.

John ya ce bayan samun kira daga al’ummar yankin ne ’yan sanda suka kai samame inda suka samu mutanen sun kai wanda ake zargin fadar basaraken yankin.

Ana zargin malami da azabtar da ɗalibi kan shan mangwaro a makaranta NAJERIYA A YAU: Matakan Kariya Daga Cutar Ƙyandar Biri

Ya ce ’yan sanda sun je fadar inda a suka yi awon gaba da wanda ake zargin zuwa hedikwatarsu ta jihar, kuma Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Baba Mohammed Azare, ya sa a gudanar da bincike kan lamarin.

Ya ce a yayin bincike “wanda ake zargin ya yi ikirarin cewa shi mamba ne a kungiyar kwararrun maharba, amma ana ci gaba da bincike domin gano gaskiyar da kuma haƙiƙanin manufarsa, in ji John.

Jami’in ya kara da cewa mutum na biyun kuma ’yan sanda ne suka kama shi ɗauke da karamar bindigar hannu a wani shigen bincike a kan hanyar Ikot Udoma da ke yankin Eket.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda shekara 65

এছাড়াও পড়ুন:

An kama mataimakin shugaban Sudan ta Kudu

An kama mataimakin shugaban ƙasa na farko a Sudan ta Kudu Riek Machar a babban birnin ƙasar Juba, a yayin da ake ci gaba da samun ƙaruwar zaman tankiya tsakaninsa da Shugaba Salva Kiir.

Faɗa tsakanin dakarun da ke goya wa shugabannin biyu baya ya tsananta a yankunan Rejaf da ke kudancin Juba da Wunaliet da ke yammaci.

Rahotanni sun bayyana cewa an kama shi ne tare da uwargidansa Angekina Teny.

Ana samun fargabar cewa kama shi zai iya kawo tarnaƙi ga yarjejeniyar zaman lafiya ta ƙasar.

Kama Machar na zuwa ne bayan shafe makonni ana samun tashe tashe hankula bayan shugaba Kiir ya tsare wasu daga cikin abokan Machar a farkon watan nan.

Tawagar majalisar ɗinkin duniya da ke Sudan ta Kudu tayi gargaɗin cewa ƙasar na cikin barazanar sake faɗawa cikin yaƙi, inda ta buƙaci ɓangarorin biyu suyi aiki da yarjejeniyar zaman lafiya ta 2018.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Isuhu Yellow a Zamfara
  • Sallah: Yadda ake shirin caɓa ado duk da tsadar kaya
  • An kama mataimakin shugaban Sudan ta Kudu
  • Lakurawa sun kashe jami’an Kwastam 2 a Kebbi
  • Kwara Ta Gargadi Jama’a Akan Gine-Gine Akan Bututun Ruwa
  • An kama mutum 3 kan zargin sata da ƙone gidan bature a Gombe
  • Duniyarmu A Yau: Ranar Qudus Ta Duniya Ta Shekara 1446
  • ’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa
  • Isra’ila ta kashe Falasdinawa 61 cikin sa’o’i 24
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Ƙasa Kiranye