Aminiya:
2025-02-24@11:56:01 GMT

Yadda jama’a suka kama ɗan shekara 65 ɗauke da bindiga

Published: 24th, February 2025 GMT

Al’ummar gari sun wani ɗan shekara 65 dauke da bindiga sun damƙa shi a hannun hukumar ’yan sanda.

Rundunar ’yan sandan Jihar Akwai Ibom ta kama mutumin ne tare da wani abokinsa da bindiga kirar ‘Double Barrell’ da harsasai da cocila da sauran kayayyaki a cikin wata kakar matafiya.

Kakakin rundunar, DSP Timfon John, ya ce dubun dan shekara 65 din mai suna Nehemiah Sunday Udo ne a ranar Asabar baya al’ummar kauyen Ekpene Obo da ke Ƙaramar Hukumar Esit Eket sun ritsa shi.

John ya ce bayan samun kira daga al’ummar yankin ne ’yan sanda suka kai samame inda suka samu mutanen sun kai wanda ake zargin fadar basaraken yankin.

Ana zargin malami da azabtar da ɗalibi kan shan mangwaro a makaranta NAJERIYA A YAU: Matakan Kariya Daga Cutar Ƙyandar Biri

Ya ce ’yan sanda sun je fadar inda a suka yi awon gaba da wanda ake zargin zuwa hedikwatarsu ta jihar, kuma Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Baba Mohammed Azare, ya sa a gudanar da bincike kan lamarin.

Ya ce a yayin bincike “wanda ake zargin ya yi ikirarin cewa shi mamba ne a kungiyar kwararrun maharba, amma ana ci gaba da bincike domin gano gaskiyar da kuma haƙiƙanin manufarsa, in ji John.

Jami’in ya kara da cewa mutum na biyun kuma ’yan sanda ne suka kama shi ɗauke da karamar bindigar hannu a wani shigen bincike a kan hanyar Ikot Udoma da ke yankin Eket.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda shekara 65

এছাড়াও পড়ুন:

Fasinjoji 4 sun rasu yayin da bas ta kama da wuta a Jigawa

Mutane huɗu sun rasa rayukansu, wasu 10 kuma sun samu raunuka bayan wata motar bas ƙirar Hummer ta kama da wuta a garin Gwaram da ke Jihar Jigawa.

Lamarin ya faru da misalin ƙarfe 4 na yammacin ranar Asabar, a kusa da makarantar sakandaren gwamnati ta Government Girls Unity Secondary School da ke Gwaram.

Gobara ta ƙone gidaje, amfanin gona da dabbobi a Borno  Za a kafa ƙarin makarantu a Zariya — Abbas Tajudeen

Kakakin ’yan sandan Jihar Jigawa, SP Lawan Adam, ya tabbatar da faruwar hatsarin cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi.

Ya ce motar ta taso daga Ƙaramar Hukumar Zaki daga Jihar Bauchi zuwa ƙauyen Ribadi da ke Ƙaramar Hukumar Gwaram.

Sanarwar ta bayyana cewa motar na ɗauke da fasinjoji 44, wanda suka haɗa da manya 25 da yara 19.

Kakakin, ya ce wutar ta samo asali ne daga katifa da aka ɗaure a bayan motar, kusa da bututun fetur.

Mutum 10 da suka samu raunuka an garzaya da su asibitin Gwaram, yayin da aka ceto sauran fasinjojin ba tare da sun ji ciwo ba.

Waɗanda suka rasu sun haɗa da Zuwairah Hassan mai shekaru 40, Fatima Hassan mai shekaru biyar.

Sauran sun haɗa da Iyatale Hassan mai shekaru uku da Halima Muhammad mai shekaru 10, dukkaninsu ‘yan ƙauyen Saldiga da ke Ƙaramar Hukumar Zaki, a Jihar Bauchi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga Kan Jami’an NSCDC A Katsina
  • Ana zargin malami da azabtar da ɗalibi saboda shan mangwaro a makaranta
  • Fasinjoji 4 sun rasu yayin da bas ta kama da wuta a Jigawa
  • An kama mutum biyu kan kisan wata mata saboda maita
  • PDP ta lashe zaɓen ƙananan hukumomin Osun
  • Sibil Difens ta cafke mutum 17 kan aikata sata a Yobe
  • Sanata Katung ya damu kan yadda wasu ke ta’azzara ta’addanci a kudancin Kaduna
  • Sanata Katung ya damu kan yadda wasu ta’azzara ta’addanci a kudancin Kaduna
  • ’Yan sanda sun daƙile satar mutane, sun kama wasu 3 a Borno