Aminiya:
2025-04-17@14:45:44 GMT

Yadda jama’a suka kama ɗan shekara 65 ɗauke da bindiga

Published: 24th, February 2025 GMT

Al’ummar gari sun wani ɗan shekara 65 dauke da bindiga sun damƙa shi a hannun hukumar ’yan sanda.

Rundunar ’yan sandan Jihar Akwai Ibom ta kama mutumin ne tare da wani abokinsa da bindiga kirar ‘Double Barrell’ da harsasai da cocila da sauran kayayyaki a cikin wata kakar matafiya.

Kakakin rundunar, DSP Timfon John, ya ce dubun dan shekara 65 din mai suna Nehemiah Sunday Udo ne a ranar Asabar baya al’ummar kauyen Ekpene Obo da ke Ƙaramar Hukumar Esit Eket sun ritsa shi.

John ya ce bayan samun kira daga al’ummar yankin ne ’yan sanda suka kai samame inda suka samu mutanen sun kai wanda ake zargin fadar basaraken yankin.

Ana zargin malami da azabtar da ɗalibi kan shan mangwaro a makaranta NAJERIYA A YAU: Matakan Kariya Daga Cutar Ƙyandar Biri

Ya ce ’yan sanda sun je fadar inda a suka yi awon gaba da wanda ake zargin zuwa hedikwatarsu ta jihar, kuma Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Baba Mohammed Azare, ya sa a gudanar da bincike kan lamarin.

Ya ce a yayin bincike “wanda ake zargin ya yi ikirarin cewa shi mamba ne a kungiyar kwararrun maharba, amma ana ci gaba da bincike domin gano gaskiyar da kuma haƙiƙanin manufarsa, in ji John.

Jami’in ya kara da cewa mutum na biyun kuma ’yan sanda ne suka kama shi ɗauke da karamar bindigar hannu a wani shigen bincike a kan hanyar Ikot Udoma da ke yankin Eket.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda shekara 65

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas Ta Fadawa Iyalan Yahudawan Da Take Tsare Dasu A Gaza Kan Cewa ‘Ya’yansu Zasu Koma A Cikin Akwatunan Gawaki

Reshen soja na kungiyar Hamas wato rundunar Izzuddin Qassam, ya gargadi iyalan fursinonin yahudawan Sahyoniyya wadanda take tsare da su a Gaza kan cewa yayansu zasu koma hannunsu gawaki, saboda irin yadda HKI take kara yawaita Jefa boma-boman a kan Falasdinawa a Gaza.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto  wani mai magana da yawan dakarun yana fadar haka a wani fai-fai bidiyo da rundunar ta watsa a yanar gizo a jiya talata.

Dakarun suna kira ga iyalan yahudawan da su yi shirin karban gawakin yayansu a cikin akwatunan gawaki, wannan kuma saboda yadda jiragen yakin HKI suke kai hare-hare babu kakkautawa kan gaza ba tare da bambanta tsakanin  yara da mata da sauransu ba.

Sakon Bidiyon yana cewa (Ya ku iyalan fursinonin ku yi shirin karban gawakin yan uwanku cikin akwatunan gawaki, tare da ganin yadda naman jikinsu a tarwatse, saboda gwamnatinku ta yanke shawarar kashe su a Gaza, don haka ku jira ku gani’.

Wannan sanarwan tana zuwa ne bayan da kungiyar ta bada sanarwan cewa ta kasa samun labarin bangaren dakarun kungiyar wadanda suke kula fursinoni don sanin halin da suke ciki, don mai yuwa an halaksu.

Daga cikin fursinonin da dakarun suka rasa inda yake dai, shi ne Edan Alexander bayahude kuma ba’amerike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Kidayar Jama’a Na Kasa
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 157, Sun Ƙwato Bindigu Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Matashi ya kai kansa ofishin ’yan sanda
  • Hamas Ta Fadawa Iyalan Yahudawan Da Take Tsare Dasu A Gaza Kan Cewa ‘Ya’yansu Zasu Koma A Cikin Akwatunan Gawaki
  • Samarwa Matasa Abun Yi Shi Zai Kawo Ƙarshen Ta’addancin Boko Haram Da ‘Yan Bindiga – Zulum 
  • Jama’a sun koka kan rashin inganci shinkafar Gwamanti a Kogi
  • Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza
  • Yadda kisan mutum fiye da 50 a Filato ya tayar da ƙura
  • Sojoji sun kama ’yan bindiga 12 a Nijar
  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa