Leadership News Hausa:
2025-03-26@21:18:04 GMT

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga Kan Jami’an NSCDC A Katsina

Published: 24th, February 2025 GMT

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga Kan Jami’an NSCDC A Katsina

Rundunar ‘yansandan Jihar Katsina ta hana wani yunƙurin ‘hari da ‘yan bindiga suka kai kan jami’an NSCDC a kan hanyar Dutsinma-Kurfi a ƙaramar hukumar Dutsinma.

Kakakin rundunar, DSP Abubakar Sadiq Aliyu, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne da sanyin safiyar Lahadi, 23 ga Fabrairu, 2025. Bayan samun kiran gaggawa da misalin ƙarfe 12:57 na dare, ‘yansanda daga ofishin Dutsinma suka gaggauta kai ɗauki, wanda ya haifar da musayar wuta da ‘yan bindigar.

‘Yan Bindiga Sun Kashe Wani Mutum Tare Da Sace Mutum Biyu A Kaduna Gwamnatin Katsina Ta Kashe Naira Biliyan 5.7 Wajen Sayen Awaki 40,000 Domin Raba Wa Mata

A sakamakon haka, ‘yan bindigar sun tsere da raunukan harbin bindiga, yayin da aka samu gawar ɗaya daga cikinsu a wurin. Jami’an tsaro sun ƙara ƙaimi wajen bin sawun waɗanda suka tsere domin cafke su.

Rundunar ‘yansandan ta tabbatar da ci gaba da jajircewarta wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma a fadin jihar.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Duniyarmu A Yau: Ranar Qudus Ta Duniya Ta Shekara 1446

Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na Duniyarmu a yau shiri wanda yake kawo maku labarai masu muhummanci a makon da ya gabata, dangane da siyasa tattalin arziki zamantake tsaro da sauran, sannan mu yi masu karin bayani daga karshe mu ji ra’ayin masana dangane da su. Da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu.

////.. Madallah, masu sauraro shirinmu na yau zai yi dubi dangane da “ranar Qudus ta Duniya’ wacce aka rayata a jiya Jumma’a ce 27 ga watan Ramdan shekara ta 1446 wanda yayi dai-dai da 28 ga watan Maris shekara ta 2025 miladiyya ne aka gudanra da ranar Qudus ta duniya, a nan kasar Iran da kuma wasu kasashe da dama a duniya.

Kamar yadda kowa ya sani ranar Qudus ta duniya ta samo asali ne daga tunanin Imam Ruhullahi Khomaini (q) wanda ya kafa JMI a shekara 1979. Inda a farko-farkon nasarar juyin juya halin musulunci ya gayyana shugaban kungiyar kwatar ‘yencin Falasdinawa na lokacin (PLO) wato Yasar Arafa ya zo nan Tehran ya hadu da Jagoran juyin juya halin musulunci na kasar Iran, inda ya tabbatar  masa cewa JMI taba bayansa, tana bayan kungiyarsa, har zuwa lokacin da zasu kori yahudawa daga kasarsu.

Banda haka Imam Khomaini(q) ya kwace ofishin jakadancin HKI a nan Tehran, ya kori yahudawan daga kasar Iran sannan ya mikawa Yasar Arafad ofishin, inda aka sauke tutan HKI a ofishin aka daga tutar kasar Falasdinu. Kuma har yanzun jakadan Falasdinawa a Tehran yana nan a wannan ofishin jakadancin Falasdinu a Tehran.

A cikin wannan yanayin ne Imam Khomaini (q) ya ware ranar jumma’a ta karshe na watan Ramadan a ko wace shekara a matsayin ranar Qudus ta duniya don raya al-amarin Falasdinawa a nan kasar Iran da kuma sauran kasashen duniya.

A lokacinda dai kungiyar PLO ce take wakiltan dukkan Falasdinawa, a lokacin ba’a kafa kungiyar Hamas ko Jihadul Islami da sauransu ba. Amma gwamnatin JMI ta ci gaba da tallafawa kungiyar PLO da kuma sauran kungiyoyin Falasdinawa a cikin kasar Falasdinu da aka mamaye, ko kuma wadanda suke wajen kasar a kasashen Siriya, Libanon Masar da Jordan da sauransu.

Ranar Qudus ta duniya ba  rana ce ta tunatarda musulmi da sauran wadanda suka damu da al-amarin falasdinu a duniya kadai ba, sai dai ranar Qudus ta Duniya harka ce ta karbu a kasashen duniya da dama. Wacce take raya wannan ranar tana kuma ayyukan wadanda zasu kaiga kwatar kasar Falasdinu daga hannun yahudawan Sahyoniyya da kuma babban kawarta kasar Amurka wacce take goyon bayan HKI da duk abinda take da shi.

A dai dai lokacinda aka kafa JMI a nan kasar Iran banda, kasar Falasdinu mutanen kasar Afirka ta kudu, suna fama da gwamnatin wariya ta fararen fata yan asalin kasar Holan, wadanda tare da taimakon turawan ingila suka mamaye kasar Afirka da kudu suka kuma kaga gwamnatin wariyar launin fata a kasar a shekara 1931.

Don haka tun lokacin bakaken fatar Afrika ta kudu suke gwagwarmaya da gwamnatin wariya ta launin fata har zuwa lokafin faduwar gwamnatin wariya a shekara 1990. Aka kafa gwamnatin democradiyya a kasar Afirka ta kudu, sannan madugun gwagwarmayan yaki da gwamnatin wariya Nelson Mandela ya zama shugaban kasar Afirka ta kudu bakar fata na farko.

Don haka bayan nasarar juyin juya  halin musulunci a nan kasar Iran a shekara 1979 gwamnatin kasar ta bayyana goyon bayanta ga gwagwarmayan mutanen kasar Afirka ta kudu bakaken fata har zuwa narasa a shekara 1990.

A cikin makon da ya gabata ne jikan mandela, Mandla Mandela ya halarci taron “nuna goyon bayan Falasdinawa’ wanda aka gudanar a birnin San’aa babban birnin kasar, a dai-dai lokacinda jiragen yakin Amurak da Burtaniya suka ruwan boma-boman a kan kasar ta Yemen saboda goyon bayan da take bawa Falasdinawa a gaza, wadanda HKI ta hana a shigo da abinci da magungun cikin yankin fiye da wata gfuda a halin yanzu.

A jawabinda da ya gabatar Mandla Mandela ya ce: A wannan shekara ma muna shirin raya ranar Qudus ta duniya karo na 46, a dai-dai lokacinda lokacinda jiragen yakin HKI suka suka barin wuta da boma-bomai a kan falasdinawa a Gaza, Lebanon da Syriya. Don haka zamu ci gaba da gwagwarmayan da muke yi na kwatar wadannan yankuna, don neman adalci, da gaskiya da kuma zaman lafiya. Kamar yadda muka yi gwagwarmaya don kwatar yencin bakaken fata a kasar Afrika ta kudu daga hannun fafare fata tsiraru, wadanda suka aiwatar da mulkin wariya a kammu na tsawon shekaru kimani 60.

Mandela ya kammala da cewa, duk tare da kokarinda shaidanu kamar Batanyahu da Trump suke yi na shafe al-ummar Falasdinu daga kasarsu, da goyon bayan yahudawan Sahyoniyya a kan kasar Falasdinu da suka mamaye, tare da makaman da suke samu daga Amurka, Burtaniya da Jamus da sauransu ba, wannan ba zai taba dushe kishin kasar da Falasdinawa suke da shi a cikin zukatansu da kuma fatan da suke da shi na komawa da kuma samun yencin kasarsu a wata rana nan gaba ba.

Don haka yadda aka saba masu goyon bayan al-ummar Falasdinu a duniya, musulmi da wadanda ba musulmi ba, sun gudanar da gangami da tarurruka inda suka gabatar da jawabai daban-daban da kuma goyon bayansu ga al-ummar Falasdinu. Har’ila yau da All..wadai da HKI da Amurak da kuma kasashen yamma wadanda suke goyon bayan HKI a kan mamayar da sukewa kasar Falasdinu tun shekara 1948.

Madallah da jagorancin JKI tun Imam Khomaini(q) da kuma da kuma Imam Sayyid Aliyul Khamina’ wanda ya ke rike da tafrkin Imam Khomaini (q) kuma ya kaiga samun ci gaban da aka yi a gwagwarmayan Falasdinawa da yahudawan Sahyoniyya a HKI. Da yardar All..abinda ya rage kadanne zuwa samun yencin Falasdinawa.

Wani abinda yakamata mu sani dangane da kasar Iran kafin nasarar juyin juya halin musulunci a kasar, shi ne gwamnatin kasar Amurka tana da cikekken iko a kan sharki Muhammad Reza Phalawi, wanda suka dorashi a kan kujerar sarautar kasar Iran. Babu abinda yake yi a Iran sai abinda kasar Amurka take bukata. Mika kai da sarki sha da gwamnatinsa suka yi ga kasar Amurka ya kai ga Amurkawa basa tabuwa ko a cikin kasar Iran.

Wannan ya kai ga gwamnatin sarkin ya kafa doka wacce ake kira Kapitalacion wacce ta bawa Amurka wa mazauna Iran, wadanda yawansu ya kai kimani 70,000 rigar kariya ta gurfana a gaban kotu a kasar Iran kan duk wani laifi da suka aikata a cikin kasar.

Kafa wannan dokar na daga cikin al-amuran da suka sa Imam Khomaini (q) ya soki sarkin kan amincewa da kafa dokar, wacce ta maida Iraniyawa abin banza a gaban Amurkawa.

Amma bayan hijirar da sarkin ya tilasta masa zuwa kasashen wajen na tsawon kimani shekaru 15 daga karshe ya dawo kasar ya kuma jagorancin kifar da gwamnatin sarkin da kuma kafa JMI a Iran a shekara ta 1979.

HKI a lokacin kawar kasar Iran ce kuma tana samun goyon bayan sarkin a mamayar da takewa kasar Falasdini. Sabanin malaman addinin musulunci a kasar musamman wadanda suke birnin Qom na ilmi. AImam Khomaini (q) da dama daga cikin malaman addini a kasar Iran suna da ra’ayin tallafawa Falasdinawa kan yahudawan Sahyoniyya ton kafin ya fara gwagwarmaya da sarki sha.

A lokacinda ya sami iko a kasar kuma mun ga abinda yayi kuma yake ci gaba da yin a tallafawa Falasdinawa su sami yancin kasarsu. Su kubuta daga hannun HKI da kuma wadanda suke taimaka masu.

Jami’an gwamnatin JMI da dama sun yi shahada a kan wannan tafarkin, fitacce daga cikinsu shi ne Janar Shahid Qasim Sulaimani, wanda shugaban kasar Amurka ma ci, a zangon shugabancinsa na farko ya bada umurni aka kashe shi a kasar Iraki a ranar 3 ga watan Jenerun shekara ta 2020.

Gwamnatin JMI musamman ta hannin kwamandan rundunar Qudus shahid Kasim Sulaimani, ta tallafawa Falasdina musamman a Gaza, da horaswa da makamai da kuma sauransu zuwa matsayin da suka kai ya zuwa yanzu.  

Karfin makaman da kwarewar da Falasdinawa suka samu tare da taimakon kasar Iran ne ya sa suka kaddamar da yakin Tufan Al-aksa a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023. Kuma sun baje kolin koreawarsu a yaki a cikin wannan yakin, wanda har yanzun ake ci gaba.

Falasdinawa a Gaza sun hama sojojin HKI mamyar yan kina Gaza, har na tsawon shekara guda da watanni uku, sannan sun ci gaba da turjewa har zuwa yanzu. Sannan sauran kasashe da kungiyoyu a yankin sun taimakawa Falasdinawa a wannan yakin. A kasar Lebanon banda kwomandojojin da kungiyar Hizbulla ta rasa, a yakin Tufanul alkha sun rasa shugaban kungiyar Sayyid Hassan Nasarallah da kuma Sayyid Safiyuddin.

A halin yanzu kasar Yemen tana fafatawa da kasar Amurka da Burtaniya kai tsaye, gaba da gaban kan matsayin da ta dauka na tallafawa Falasdinawa a gaza. Daga shekara ta 2023 zuwa yanzu ta kaddamar da shahidar masu yawa kuma tana yi.

Don haka al-amarin Falasdinawa da kuma masallacin Qudus wanda HKI ta mamaye, tare da taimakon kasashen yamma ya zama ta kasa da kasa, saboda yadda aka sami wadanda suke tallafawa al-amarin ta hanyar raya ranar Qudus ta duniya da kuma wasu hanyoyi.

Kafin fara yakin Tufanul Aksa, gwamnatin HKI tana hana Falasdinawa daga tutar Falasdinu hatta a cikin kasarsu, da aka mamaye, ammam a halin yanzu da wuya a sami kasa daga cikin kasashen yamma inda ba’a daga tutar Falasdinu.

Ban haka matasa wadanda suka farka kan wannan al-amarin suna daga tutar Falasdinu har a fadar white House. Masu zanga zangar goyon bayan falasdinawa a Amurka suna daga tutar Falasdinawa har a kofar shiga fadar white House.

Wannan ba kome yake nunawa ba sai, cewa al-amarin Falasdinawa ya kai ga dole ne kasashen yamma ko suna so ko basa so nan gaba sai an kafa kasar Falasdinu a kan kasar Falasdinu da aka mamaye. Wacce birnin Qudus zai kasance babban birnin kasar.

Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu. Wassalamu alaikum warahmatullahi wa barakatuhu,

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Nigeria: An  Kashe Sojoji Da DAma A Wani Hari Da Aka Kai Wa Sansanonin Soja Biyu Hari A Jihar Borno
  •  Sojojin Sudan Sun Kwace Wuri Na Karshe Da Yake A Hannun “Rundunar Kai Daukin Gaggawa” A Cikin Birnin Khartum
  • Duniyarmu A Yau: Ranar Qudus Ta Duniya Ta Shekara 1446
  • Gidauniyar Daily Trust da WRAPA sun ’yanta fursunoni 21 a Kaduna da Katsina
  • Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdullahi Usman, ya rasu
  • Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdulahi Usman, ya rasu
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Kafa Rundunar Daukin Gaggawa Don Magance Matsalolin Tsaro
  • Harin Neman Shahada Ya Kashe ‘Dan Share Wuri Zauna Daya A Garin Haifa
  • UNICEF: Yara a Gaza suna fama da matsalar kwakwalwa da ba a taba ganin irinsa ba
  • Syria: SOHR ta fallasa jami’an tsaron sabuwar gwamnati na yi tsiraru kisan gilla