HausaTv:
2025-02-24@15:39:19 GMT

Al-Khazali: ‘Yan gwagwarmaya a Iraki za su gaba da bin tafarkin Sayyid Nasrallah

Published: 24th, February 2025 GMT

Dakarun gwagwarmaya a Iraki za su ci gaba da ayyuka bisa tafarkin babban sakataren kungiyar Hizbullah Sayyid Hasan Nasrallah, wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen kare wadanda ake zalunta, kamar yadda Qais al-Khazali, babban sakataren kungiyar Asa’ib Ahl al-Haq ya bayyana.

Da yake magana a ranar wannan Lahadin, al-Khazali ya jinjinawa Sayyed Nasrallah, yana mai bayyana shi a matsayin babban mutum wanda ya shafe tsawon rayuwarsa a tafarkin jihadi da kare wadanda ake zalunta.

Ya kara tabbatar da cewa babu makawa wa’adin Sayyed Nasrallah na samun nasara a kan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila yana zuwa.

“Mun yi alkawarin shrda ma Nasrallah cewa, za mu ci gaba da tafiya a kan wannan tafarki har zuwa lokacin da za a tsarkakae kasar Falastinu daga mamayar  gwamnatin Haramtacciyar kasar Isra’ila da yahudawan sahyuniya, in ji shi.

A cewar Hani Khater, shugaban ofishin yada labarai na Al-Ahed na kasar Iraki a ofishin Tehran, kimanin ‘yan kasar Iraki dubu 200 ne suka halarci jana’izar Sayyed Nasrallah a jiya Lahadi a birnin Beirut.

Sannan kuma Ya yi nuni da cewa, akidar Sayyed Nasrallah za ta ci gaba da dawwama a duk fadin yankin gabas ta tsakiya da ma duniya baki daya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Sayyed Nasrallah

এছাড়াও পড়ুন:

Lebanon: An Rufe Shahid Sayyid Hassan Nasrallah A Makwancinsa Na Karshe A Birnin Beirut

Lokacin kadan da ya gabata ne dai aka rufe shahid Sayyid Hassan Nasrallah a makwancinsa na kare dake kusa da filin saukar jiragen sama na Beirut,bayan da aka dauki tsawon yau ana gudanar da jana’izarsa.

Dubun dubatar mutanen Lebanon da kuma wasu daga wajen kasar ne su ka halarci taron jana’izar Sayyid Shahid Hassan Nasrallah da kuma ta Sayyid Hashim Safiyuddin da  aka gudanar a cikin birnin Beirtu.

Tashar talabijin din al’mayadin ta bayyana cewa bisa kirdado adadin mutanen da su ka halarci jana’izar sun kai mutane miliyan daya da 400,000.

Mahalarta jana’izar sun cika filin wasa na birnin Beirut da kuma manyan tituna ta yadda babu masaka cinke, da hakan ya sa motar da take dauke da makararsa da kuma ta Sayyid Hashim Safiyuddin ta rike tafiya a cikin nawa.

An fara gudanar da taron jana’izar ne dai da takaitattun jawabai daga wakilin jagoran juyin musulunci na Iran da kuma na babban sakataren kungiyar ta Hizbullah Sheikh Na’im Kassim.

A tsawon lokacin da motar dake dauke da makarar Sayyid Shahid take tafiya an rika watsa jawaban Shahidin da ya yi a lokuta mabanbanta a tsawon rayuwarsa da suke da alaka da yin jinjina ga al’ummar Lebanon,musamman masu bai wa gwgawarmaya kariya da goyon baya.

Lokaci kadan da ya gabata ne dai aka shigar da makarar da take da Sayyid Hassan Nasarallah cikin makwancinsa na karshe, a daidai lokacin da ake karanta suratu Yasin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta yi Allah wadai da keta hurumin kasar Lebanon da Isra’ila ta yi
  • Pezeshkian: Hizbollah tana nan a raye a kan tafarkin gwagwarmaya
  • Hamas ta yaba da irin goyon bayan da Sayyed Nasrallah ya baiwa Falasdinu
  • Tawagar Iran a Beirut ta gana da shugabannin Lebanon
  • Lebanon: An Rufe Shahid Sayyid Hassan Nasrallah A Makwancinsa Na Karshe A Birnin Beirut
  • Sheikh Kassim: Gwagwarmaya Za Ta Ci Gaba Da Dukkanin Karfinta
  • Wakilin Jagoran Juyi A Wurin Jana’izar Sayyid: Gwgawarmaya Za Ta Ci Gaba
  • Sojojin Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Luguden Wuta Kan Gabar Yammacin Kogin Jordan
  • Tawagogi Na Isa Lebanon Domin Halartar Jana’izar Sayyed Hassan Nasrallah