Iran ta yi Allah wadai da keta hurumin kasar Lebanon da Isra’ila ta yi
Published: 24th, February 2025 GMT
Iran ta yi kakkausar suka kan ta’addancin Isra’ila game da keta hurumin kasar Lebanon, bayan da jiragen yakinta suka yi shawagi a yankin da ake gudanar da jana’izar tsoffin shugabannin kungiyar Hizbullah.
A wani sako da ya wallafa a shafin sada zumunta a daren Lahadi, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmaeil Baghaei, ya ce gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta shiga wani sabon yanayi na kara tabbatar wa duniya da cewa ita bata bin dokokin kasa da kasa.
Baghaei ya ce jiragen yakin haramtacciyar kasar Isra’ila sun yi kokarin tarwatsa dubban daruruwan ‘yan kasar Lebanon da wasu da suka taru domin nuna girmamawa ga jarumtansu, shugaban kungiyar Hizbullah Sayyed Hassan Nasrallah da mataimakinsa da suka nada Sayyed Hashem Safieddine.
Baghaei ya yi kira ga kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ya yi Allah wadai da wannan mataki na rashin da’a, da rashin girmamam dokokin duniya da Isra’ila ta nuna a jiya a lokacin janazar Sayyid Hassan Nasrullah a Beirut.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Bukaci Hanzarta Hukunta Shugabannin ‘Yan Sahayoniyya Kan Laifukan Da Suka Aikata
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya yi kira da a gaggauta bibiyar bayanan manyan laifuka na shugabannin gwamnatin mamayar Isra’ila
A wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na kasar Holland, ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya yi Allah wadai da ci gaba da mamaya da kuma laifukan da yahudawan sahayoniyya suke yi a Falasdinu, tare da yin kira ga kasashen duniya da su dauki matakin gaggawa wajen hanzarta bibiyar bayanan shari’a da laifuka a kotunan duniya dangane da kisan kiyashi da laifukan yaki da shugabannin mamayar Isra’ila suka aikata.
Kamfanin dillancin labaran Fars ya habarta cewa: Ministan harkokin wajen kasar Holand Caspar Veldkamp da takwaransa na Iran Abbas Araqchi sun tattauna kan batutuwan da suka shafi kasashen biyu da ci gaban kasa da kasa a wata tattaunawa ta hanyar wayar tarho a jiya Asabar.
Haka nan kuma yayin da yake ishara da dogon tarihin dangantakar da ke tsakanin Iran da Netherlands, ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye ta ke ta gudanar da dukkanin harkokin da suka shafi kasashen biyu bisa mutunta juna da moriyarsu.