Aminiya:
2025-04-19@06:12:30 GMT

Matar aure ta banka wa mijinta wuta

Published: 24th, February 2025 GMT

An gurfanar da wata matar aure a kotu kan zargin ta da cinna wa mijinta wuta a Jihar Kano.

Ana zargin matar ta watsa wa mijin nata fetur sannan ta cinna masa wuta ne saboda ya shiga dakin sabuwar amaryarsa, suna tattaunawa da ita.

Shaidu sun bayyana cewa wadda ake zargin ta yi aika-aikan ne bayan ta nemi mijin nata ya fito daga dakin amaryar tasa amma ya ƙi amincewa.

Magidancin ya samu munanan kuna a sakamakon wutar da matar tasa ta yi masa.

Lauyar Gwamantin Jihar Kano, Saima Garba, ta karanta wa matar takardar tuhumar aikata kisa da ake mata, amma ta musa.

Daga nan alƙalin kotun Majistare mai Lamba  25, Halima Wali, ta ba da umarnin tsare matar a gidan yari sannan ta ɗage sauraron shari’ar da makonni biyu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Amarya matar

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta Bada Tabbacin Tsaro A Bukin Ista

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Gombe, Bello Yahaya ya bayar da umarnin tura isassun jami’ai a fadin jihar domin samar da isasshen tsaro kafin bukin Easter, da kuma bayan bikin Easter.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar a Gombe.

 

A cewarsa, an tura jami’an dabarun dakile hare-hare zuwa muhimman wuraren da suka hada da wuraren ibada, wuraren shakatawa, kasuwanni, da sauran wuraren taruwar jama’a.

 

Ya kuma ce, kungiyoyin sintiri da jami’an tsaron cikin za su kasance a kasa domin sanya ido kan ayyukan da kuma gaggauta daukar matakin magance duk wata matsala idan ta taso.

 

Kwamishinan ya lura cewa rundunar tana aiki tare da hadin gwiwar ‘yan uwa jami’an tsaro da masu ruwa da tsaki a cikin al’umma domin kula da su a cikin doka da oda yayin da ake ƙarfafa ‘yan ƙasa su kasance masu bin doka da oda kuma su kai rahoton duk wani abin da ake tuhuma ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa.

 

HUDU/GOMBE

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cutar Da Ke Kassara Gonakin Tumatir Ta Sake Bulla A Jihar Kano
  • China Ta Musanta Zargin Ukraine Na Tallafawa Rasha Da Makamai
  • Ya kashe masoyin tsohuwar matarsa bayan sakinta a Neja
  • Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta Bada Tabbacin Tsaro A Bukin Ista
  • Matar gwamna ta ɗauki nauyin ragon suna da hidimar duk matar da ta haifi ’yan uku a Sakkwato
  • Hamas ta gabatar da shawara kan yarjejeniyar musayar fursunoni da tsagaita wuta
  • Sojojin Nijeriya Sun Yi Lugudan Wuta Kan Sansanin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Taron Ƙarawa Ma’aikatan Jinƙai Sani A Jihar Kano
  • Zargin Ganduje: Za mu sanar da lokacin yanke hukunci —Kotu
  • Matashin Da Ya Ƙware Wajen Kashe Mutane Da Ƙwace Ya Miƙa Kansa Ga ‘Yansanda A Kano