Gwamnatin jihar Jigawa ta bayyana jin dadinta bisa gagarumin nasarorin da aka samu wajen aiwatar da manufofinta guda 12 don inganta rayuwar al’umma da ma ci gaban jihar baki daya.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan a yayin taron wayar da kan jama’a da aka gudanar a karamar hukumar Birnin Kudu.

Ya bayyana cewa shirin da ke da nufin kusantar da jama’a ga gwamnati, zai kuma tabbatar da cewa manufofi da shirye-shiryen da aka aiwatar sun dace da  muradin al’umma.

Don haka Namadi ya yabawa al’ummar yankin bisa yadda suka rungumi ayyukan da gwamnatin jihar ke  aiwatarwa hannu bibbiyu, tare da yin alwashin ci gaba da samar da ingantattun ayyuka.

Gwamnan ya kuma ba da tabbacin cewa, zai yi nazarin takardar da Farfesa Abubakar Sani Birnin Kudu ya gabatar mai kunshe da bukatun al’ummar karamar hukumar ta Birnin Kudu.

Shi ma da yake jawabi kwamishinan ayyuka da sufuri na jihar Injiniya Gambo S. Mallam ya ce gwamnatin jihar ta bada kwangilar sake gina hanyar Birnin Kudu zuwa Sundimina zuwa Kiyawa, akan kudi naira biliyan 11 da miliyan 500.

A cewarsa, aikin zai hada da sanya kwalta, da gina gadoji da magudanan ruwa, da sauran abubuwan da suka kamata.

Injiniya Gambo ya yi nuni da cewa, a halin yanzu gwamnatin jihar na gudanar da ayyukan tituna da dama a karamar hukumar Birnin Kudu.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, gwamnan farar hula na farko a jihar Alhaji Ali Sa’ad Birnin Kudu ne ya kaddamar da aikin sake gina hanyar ta Birnin Kudu zuwa Sundimina, zuwa Kiyawa a hukumance.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Ahmad Lawan ya raba tallafin N27m da buhun shinkafa 300 a Yobe

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Lawan, ya bayar da gudummawar Naira miliyan 27 da buhunan shinkafa 300 ga mutanen da gobara ta shafa a ƙananan hukumomi uku da ke mazaɓarsa a Jihar Yobe.

Ƙananan hukumomin da abin ya shafa sun haɗa da Machina, Nguru, da Yusufari.

An kama mutum 3 kan zargin sata da ƙone gidan bature a Gombe Tsohon hadimin gwamnan Kano, Abdullahi Tanka Galadanci, ya rasu

Sanata Lawan, ya jajanta wa mutanen da suka yi asarar dukiya sakamakon gobarar.

Ya ce haƙƙinsu ne su taimaka wa juna, kuma zai ci gaba da ƙoƙari don ganin cewa wadanda abin ya shafa sun samu tallafin da ya dace.

Ya bayyana cewa wannan tallafin zai ƙara ƙaimi ga ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke yi na samar da agajin gaggawa ga mutanen da abin ya shafa, tare da taimaka musu, su farfaɗo daga ɓarnar da gobarar ta yi musu.

A cewarsa, an ware Naira miliyan 12 da buhunan shinkafa 150 ga Ƙaramar Hukumar Machina, wanda za a raba a garuruwan Ngabarawa, Dole, Ghana, da Damai.

Ƙaramar Hukumar Nguru, za ta karɓi Naira miliyan biyar da buhunan shinkafa 50, wanda za a raba wa al’ummar Askema da Mirba.

Ƙaramar Hukumar Yusufari, za ta samu Naira miliyan 10 da buhunan shinkafa 100, wanda za a raba wa mutanen Tulo-Tulo da Isufuri.

Sanata Lawan, ya buƙaci gidauniyar SAIL Foundation, wacce ke kula da rabon tallafin, da ta tabbatar da gaskiya da adalci wajen raba wa waɗanda suka cancanta.

Ya kuma yi addu’a Allah Ya ba waɗanda abin ya shafa ikon jure wannan jarabta da sauƙi a gare su, musamman a wannan wata mai alfarma na Ramadan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Bada Hutun Sallah Karama Ta 2025/1446
  • Za a Fara Cin Moriyar Shirin BEAR III Na UNESCO da Koria Ta Kudu Jihar Kano
  • Kwara Ta Gargadi Jama’a Akan Gine-Gine Akan Bututun Ruwa
  • NLC a Zamfara sun Bada Wa’adin Kwanaki 14 a Aiwatar da Mafi Karancin Albashi
  • Kantoman Ribas ya dakatar da hadiman Fubara
  • Ahmad Lawan ya raba tallafin N27m da buhun shinkafa 300 a Yobe
  • Gwamnatin Kano za ta hukunta masu shigar banza a bikin Sallah
  • Kamfanin BYD Ya Samu Karin Ribar Kaso 34 Zuwa Dala Biliyan 5.6 A Bara
  • Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren Gwamnati
  • NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi