Galadima Muri, na Masarautar Muri, kuma Hakimin Jalingo, Alhaji Lamido Abba Tukur, ya yi kira ga manoma da ‘yan kasuwa a Taraba da su yi la’akari da halin da talakawa ke ciki, su rage farashin kayan abinci.

Ya yi wannan kiran ne a yayin cikarsa shekaru 40 akan karagar mulki a matsayin Galadima a Jalingo.

Basaraken  ya nuna damuwarsa kan yadda hauhawar farashin kayayyakin abinci a kullum ke kara ta’azzara, da kuma kalubalen tattalin arziki da talakawa ke fuskanta.

Galadiman ya yabawa gwamna Agbu Kefas kan yaki da matsalar tsaro a Taraba, inda ya bayyana ci gaban da aka samu a shekarun baya-bayan nan a matsayin abin a yaba.

“Amincewa da gudanar da wannan biki na cika shekara 40 akan karagar mulki a matsayin Galadima a yau, ya biyo bayan yakin da Gwamna Kefas ya yi da wajen tabbatar da ganin an shawo kan matsalar tsaro a Taraba, tare da wanzar da zaman lafiya, ba a Jalingo kadai ba, har ma a jihar Taraba baki daya, wanda ya baiwa jama’a damar samun hanyoyin samun kudaden shiga na yau da kullum“. Inji shi.

“A matsayina na babasaranaina shiga cikin damuwa matuka a duk lokacin da jama’ata suka gaza shiga gonakinsu ko gudanar da  sana’o’insu saboda rashin tsaro. Ina son in yaba wa gwamna Agbu Kefas bisa gaggarumin yaki da rashin tsaro a Taraba, wanda sannu a hankali ana samun kwanciyar hankali a halin yanzu.

Tun da farko, shugaban taron, Alhaji Kabiru Marafa, da Lamido Bakundi, mai martaba Alhaji Kabiru Muhammad Gidado Misa, sun bayyana Galadima a matsayin basarake abin koyi, wanda ake alfahari da ayyukansa da jagororinsa.

Jamila Abba

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Alamar Deepseek” Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya

Sai dai, tabbas za a karya tsarin, ganin yadda ba a samun adalci a ciki. Mun san kasar Sin daya ce daga cikin kasashen da suka warware dabaibayin hana ci gaba da kasashen yamma suka daura musu, inda ta raya tattalin arzikinta, tare da taka muhimmiyar rawa a cikin tsarin duniya ta fuskar samar da kayayyaki.

Daga bisani me kasar Sin ta yi? Ta samar da tunanin gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya, inda aka nanata bukatar ba sauran mutane damar jin dadin zaman rayuwa, matukar wani mahaluki na son samun zaman rayuwa mai inganci. Bisa wannan tunani ne, kasar Sin ta samar da jerin shawarwari masu alaka da ci gaban tattalin arziki, da tsaro, da cudanyar mabambantan al’adu a duniya, da tsayawa kan manufofin tattaunawa tare, da gudanar da aikin gini tare, da raba moriya, gami da sanya kowa a turbar samun biyan bukata, ta yadda kasar ke ta samun amincewa da goyon baya daga karin kasashe.

Tunanin al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya, da manhajojin AI na “open source”, duk sabbin dabarun daidaita al’amura ne. A lokacin da wani tsohon abu ya gaza biyan bukata, ya kamata a gwada wani na sabo. Ko ba haka ba?(Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Na Adawa Da Kara Yawan Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Amurka Ta Takaita Fitar Da Kayayyakinsu
  • Majalisa ta buƙaci a rage kuɗin data don sauƙaƙa wa ’yan Najeriya 
  • Zamu Tabbatar Ingantuwar Depon Sojoji Na Zaria – Ministan Tsaro Badaru
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata a matsayin hutun salla
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata a matsayin hutun sallaGwamnati Ta Ayyana 31 Ga Maris Da 1 Ga Afrilu A Matsayin Ranakun Hutu Don Bukin Eid-el-Fitr Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 31 ga Maris, da Talata, 1 ga Afrilu, a matsayin ranakun hu
  • DAGA LARABA: Yadda Farashin Kayan Masarufi Suke Gabanin Sallah
  • Nijeriyar Jiya Da Yau: Kiki-Kakar Sabgar ‘Yan Majalisu
  • Alamar Deepseek” Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya
  • An Ɗauko Sojoji Daga Waje Don Horas Da Dakarun Nijeriya 
  • An Ɗauko Sojoji Daga Wajen Don Horas Da Dakarun Nijeriya