Mun gano inda Bello Turji ya ɓoye —Sojoji
Published: 24th, February 2025 GMT
Babban Jami’in Ayyuka na Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya, Manjo-Janar Emeka Onumajuru, ya bayyana cewa saura kiris su gama da jagoran ’yan ta’adda, Bello Turji.
Manjo-Janar Emeka Onumajuru ya bayyana cewa sojojin suna kan bibiyar motsin Bello Turji, kuma sun gano inda yake, amma bai yi ƙarin bayani ba.
“Babu wani kwan-gaba-kwan-baya a wurin sojoji kan maganar Bello Turji, mun gano inda maɓoyarsa take,” in ji Janar Emeka.
Ya ci gaba da cewa a halin yanzu sojoji sun riga sun rutsa Turji a maɓoyarsa, babu inda zai iya motsawa ya je, saboda tsoro
Ya bayyana haka ne a safiyar Litinin yana mai cewa kwanakon Turji sun kusa karewa.
Janar din ya bayyana haka ne a yayin hirar da gidan talabijin na Channels ya yi da shi a ranar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Maboya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Bayyana Karfafa Matasa A Matsayin Jigon Ayyukan Gwamnatinsa
Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya jaddada kudirinsa na karfafawa matasa sana’o’i da ayyukan yi a jihar.
Ya bayyana haka ne a yayin bikin bude wani katafaren shago da wani bawan Allah ya gina a kan titin Malam-Madori a karamar hukumar Hadejia.
Ya bayyana cewa, bai wa matasa damar yin sana’o’i shi ne jigon tsare-tsaren gwamnati mai dauke da manufofi 12, da ke da nufin daukaka jihar zuwa matsayi mafi girma.
A cewarsa, daya daga cikin ginshikan tsare-tsaren gwamnatinsa shi ne samar da damammaki da ke bai wa matasa sana’o’in dogaro da kai, domin samun ci gaba a kasuwar hada-hadar kudi.
Gwamna Namadi ya ce, gwamnatin jihar ta kaddamar da kafa shaguna da za a rika sayar da kayayyaki a farashi mai rahusa a fadin jihar domin amfanin al’umma.
Don haka Gwamnan ya yaba da kafa wannan katafaren shago a garin Hadejia, inda ya bayyana shi a matsayin gudunmawa kuma abin yabawa ga al’umma.
Ya bayyana shi a matsayin wani muhimmin abu da zai samar da ayyukan yi, musamman ga matasa.
Namadi, ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na tallafawa daidaikun mutane da ‘yan kasuwa da ke ba da fifiko wajen inganta rayuwar al’umma.
“Za mu ci gaba da karfafa wa wadanda suka nuna kwazo wajen kyautata rayuwar jama’armu da ci gaban al’ummarmu. Inji shi.
Usman Muhammad Zaria