Sojojin Sudan Sun Kace Birnin El-Obeid Daga Hannun RSF
Published: 24th, February 2025 GMT
Sojojin Sudan sun ce sun kawo ƙarshen iko da birnin el-Obeid na yankin kudancin ƙasar na kusan shekaru biyu da dakarun RSF suka yi.
Wannan nasara na zuwa ne ‘ƴan sa’o’i bayan da RSF ta rattaɓa hannu kan yarjejeniyar siyasa a Nairobi da ke ƙasar Kenya na kafa gwamnatin aware a yankunan da ke ƙarƙshin ikonta.
Tun dai shekarar 2023 ne rundunar RSF da sojojin Sudan ke fafatawa, inda dubban fararen hula ke mutuwa sannan da dama na barin gidajensu.
Rikicin dai ya raba ƙasar ɓangarori biyu, inda sojoji ke iko da arewa da gabashi, yayin da su kuma RSF ke iko da mafi yawancin yankin Darfur da ke yammaci da wasu sassan kudanci.
Birnin El-Obaid dai wanda shi ne babban birnin jihar Kordofan, yana da matuƙar muhimmanci ga Khartoum, babban birnin ƙasar. Wannan ne wani yunƙuri na sojoji a ƴan makonnin nan tun bayan kame yankuna da dama na Khartoum daga hannun RSF.
Al’ummar Sudan sun fito tituna suna ta bayyana farin cikinsu dangane da sake ƙwato birnin daga hannun waɗanda suke bayyanawa a matsayin ƴan tawaye.
Wata mai fafutuka ƴar ƙasar Sudan, Dallia Abdlemoniem ta shaida wa BBC cewa ƙwace iko da birnin daga hannun RSF “gagarumar” nasara ce.
Ta ƙara da cewa sojoji na ci gaba da shirin kutsawa yammaci inda a can ne mayaƙan na RSF suke.
Dukkannin ɓangarorin biyu na sojojin gwamnati da na rundunar mayaƙan RSF sun musanta zarge-zargen take haƙƙin bil’ada da aka yi musu, da har ta kai Amurka ta ƙaƙaba wa jagororinsu takunkumai. Bugu da ƙari, an zargi RSF da aikata laifukan kisan ƙare dangi a Darfur.
An soki ƙasar Kenya bisa karɓar ɓakuncin da ta yi makon da ya wuce da ke son kafa gwamnatin ƴan aware.
Da ma dai gwamnatin sojin Sudan ta gargaɗi Kenya da cewa za ta yi ramuwar gayya kan Kenyar bisa matakin, kuma tuni ta yi wa jakadanta da ke Nairobi kiranye.
Sai dai a wani martani da suka yi, ministan harkokin wajen Kenya ya ce babu “wata mummunar manufa” a “bai wa dukkan ɓangarorin da ke rikici da juna dama.
bbc
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Birtaniya Da Faransa suna Son Aikewa Da Sojojin Turai 30,000 Kasar Ukiraniya
Jaridar Wall Satreet Journal ta ambaci cewa kasashen Faransa da Birtaniya suna shirya yiyuwar aikewa da sojojin tabbatar da zaman lafiya a cikin kasar Ukiraniya idan an tsagaita wutar yaki.
Jaridar ta Amurka ta kuma kara da cewa; Idan an kai ga cimma tsagaita wutar yaki to da akwai yiyuwar turawan za su aike da sojojin zaman lafiya da za su kai 30,000 daga cikin har da na kasar Switzerland.
Sai dai kuma aiwatar da shirin na turai yana da alaka ne da yadda Donald Trump zai amince da kasarsa ta taka rawa, idan har Rasha ta kai wa turawan hari, ko ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta, kamar yadda jaridar ta ambato wani jami’in turai din yana fada.
Jaridar ta kara da cewa turawan ba za su bukaci Amukan ta aike da sojoji tare da su zuwa Ukiraniya din ba, sai dai za su bukaci taimakonta da kayan aikin da ba su da su.
A ranar Alhamis mai zuwa ne ake sa ran cewa Fira ministan Birtaniya Sir Keir Rodney Starmer zai tattauna shirin nasu na turai da shugaban kasar Amurka Donald Trump.
A gefe daya, kwamandan sojojin kasar Switzerland Laftanar Janar Thomas Sussli ya bayyana cewa, kasarsa za ta iya taimakawa da wani adadi na sojojin zaman lafiya anan gaba,idan har gwamnatin Ukiraniyan ta bukaci hakan.