Jam’iyyar NNPP reshen jihar Kano ta dakatar da ‘yan majalisar tarayya huɗu bisa zargin aikata abubuwan da suka saɓa wa manufofin jam’iyya. Shugaban jam’iyyar a jihar, Alhaji Hashimu Dungurawa, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a Kano a ranar Litinin.

Waɗanda aka dakatar sun hada da Kawu Sumaila (Sanatan Kano ta Kudu), Ali Madakin Gini (Dala), Sani Rogo (Rogo/Karaye), da Kabiru Rurum (Rano/Kibiya).

Dungurawa ya ce waɗannan ‘yan majalisa sun samu tikitin NNPP ne, amma daga baya suka fara aikata abubuwan da suka sabawa jam’iyyar.

Nan Kusa Ƴan Majalisun NNPP Za Su Koma APC – Ganduje  Jam’iyyar NNPP Daya INEC Ta Amince Da Ita – Shugaban Jam’iyyar 

Ya ce misali, Sanata Sumaila ya ƙaddamar da wasu ayyuka a jami’arsa ba tare da ya gayyaci wakilan jam’iyyar ba, wanda hakan ya nuna alamun yi wa NNPP zagon ƙasa. Shugaban jam’iyyar ya ƙara da cewa za a kafa kwamitin bincike domin tantance lamarin da ɗaukar matakin da ya dace.

Sai dai Dungurawa ya ce har yanzu jam’iyyar na da shirin sasanta matsalar, inda ya bayyana cewa idan waɗanda aka dakatar suka gyara dangantakarsu da jam’iyya, za a iya dawo da su. Wannan matakin na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun rahotannin rikicin cikin gida a NNPP, inda wasu mambobi ke kukan ana ware su daga harkokin jagoranci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Matuƙar Abdullahi Abbas Ya Cigaba Da Zama Shugaban APC A Kano, Zan Fita – Ata

Matuƙar Abdullahi Abbas Ya Cigaba Da Zama Shugaban APC A Kano, Zan Fita – Ata

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Hamas Ta Dakatar Da Tattaunawa Da HKI Har Zuwa Sakin Fursinoni Falasdinawa
  • Ministan Gidaje, Ba Ɗan Jam’iyyar APC Ba Ne – Shugaban APC Na Kano
  • Kotun Tarayya Ta Dakatar Da Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Daga Tsige Honarabul Ango
  • Da Ɗumi-ɗumi: NNPP Ta Dakatar Da Sanata Kawu Sumaila Da Wasu ‘Yan Majalisa Uku
  • NNPP ta dakatar da Kawu Sumaila da Ali Madakin Gini
  • Matuƙar Abdullahi Abbas Ya Cigaba Da Zama Shugaban APC A Kano, Zan Fita – Ata
  • Gawuna ne ya lashe zaɓen Gwamnan Kano a 2023 — Ata
  • PDP ta lashe zaɓen ƙananan hukumomin Osun
  • Jakadan Kasar Sin Ya Bukaci Dakatar Da Duk Wani Tashin Hankali A Gabashin Kongo