NNPP Ta Dakatar da ‘Yan Majalisa Huɗu Bisa Zargin Yi Wa Jam’iyya Zagon Ƙasa
Published: 24th, February 2025 GMT
Jam’iyyar NNPP reshen jihar Kano ta dakatar da ‘yan majalisar tarayya huɗu bisa zargin aikata abubuwan da suka saɓa wa manufofin jam’iyya. Shugaban jam’iyyar a jihar, Alhaji Hashimu Dungurawa, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a Kano a ranar Litinin.
Waɗanda aka dakatar sun hada da Kawu Sumaila (Sanatan Kano ta Kudu), Ali Madakin Gini (Dala), Sani Rogo (Rogo/Karaye), da Kabiru Rurum (Rano/Kibiya).
Dungurawa ya ce waɗannan ‘yan majalisa sun samu tikitin NNPP ne, amma daga baya suka fara aikata abubuwan da suka sabawa jam’iyyar.
Ya ce misali, Sanata Sumaila ya ƙaddamar da wasu ayyuka a jami’arsa ba tare da ya gayyaci wakilan jam’iyyar ba, wanda hakan ya nuna alamun yi wa NNPP zagon ƙasa. Shugaban jam’iyyar ya ƙara da cewa za a kafa kwamitin bincike domin tantance lamarin da ɗaukar matakin da ya dace.
Sai dai Dungurawa ya ce har yanzu jam’iyyar na da shirin sasanta matsalar, inda ya bayyana cewa idan waɗanda aka dakatar suka gyara dangantakarsu da jam’iyya, za a iya dawo da su. Wannan matakin na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun rahotannin rikicin cikin gida a NNPP, inda wasu mambobi ke kukan ana ware su daga harkokin jagoranci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
‘Yansanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin Ɓarayin Wayar Wutar Lantarki Ne A Yobe
Rundunar ‘yansandan jihar Yobe ta kama wasu mutane biyu da ake zargin barayin wayar wutar lantarki ne a Damaturu babban birnin jihar. Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, SP Dungus Abdulkarim, a wata sanarwa da ya fitar, ya bayyana cewa, rundunar ‘yansanda ta Karasuwa ce ta kama wadanda ake zargin – Yahaya Mustapha, 28, da Bello Yakubu, 38, da misalin karfe 1:00 na rana a ranar 12 ga watan Afrilun 2025. ‘Yansanda Sun Gano Haramtaccen Wurin Haɗa Makamai A Kano Hatsarin Mota Ya Hallaka Mutum Ɗaya A Bauchi, Wasu Sun Jikkata Abdulkarim ya ce, wadanda ake zargin sun fito ne daga unguwar Takari da ke karamar hukumar Gashua Bade a jihar, an kama su ne da manyan igiyoyin wutar lantarki a kauyen Waro da ke karamar hukumar Karasuwa. A cewar sanarwar, an kama wadanda ake zargin ne a lokacin da suke loda igiyoyin a kan keke-napep mai kafa uku. Kwamishinan ‘yansandan jihar, CP Emmanuel Ado ya jaddada kudirin rundunar na yaki da masu aikata miyagun laifuka da barnata dukiyoyin jama’a, inda ya bukaci jama’a da su sanya ido tare da kai rahoton duk wasu zarge-zarge ko wasu mutane da ke shirin barnata kadarorin jama’a. Ya kuma yabawa ‘yan jihar bisa yadda suke bayar da sahihan bayanai, wanda hakan ya taimaka wajen bunkasa kokarin rundunar.Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp