Babbar kotun tarayya da ke Gusau a jihar Zamfara ta dakatar da majalisar dokokin jihar daga tsige Honarabul Aliyu Ango Kagara, dan majalisar APC mai wakiltar mazabar Talata Mafara ta Kudu.

A wata sanarwa da Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar APC na Zamfara, Yusuf Idris Gusau ya fitar, ya bayyana cewa hukuncin ya biyo bayan wata kara mai lamba FHC/GSCS/10/2025 da Kagara ya shigar kan Majalisar Dokokin Jihar Zamfara,  da Kakakinta, da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC).

Ta ce shari’ar da mai shari’a Salim Olasupo Ibrahim ya jagoranta ta kalubalanci tsige Kagara da shugabannin majalisar suka yi.

A cewar sanarwar, kotun ta bayar da umarnin wucin gadi na hana INEC gudanar da zaben cike gurbi na mazabar Talata Mafara ta Kudu, wanda Kagara ke wakilta a halin yanzu.

Mai shari’a Olasupo ya kuma bayar da umarnin tsayawa kan wannan hukunci har zuwa lokacin da za a ci gaba da sauraron karar da aka shigar a gaban kotu.

An dage sauraron karar zuwa ranar 12 ga watan Maris na 2025.

A halin da ake ciki, majalisar dokokin jihar Zamfara ta dakatar da ‘yan majalisa 9 da suka fito daga jam’iyyu daban daban, lamarin da ya rage yawan mambobinta da ke kasa da kashi biyu bisa ukun da ake bukata wajen zartar da kudiri.

Duk wata doka da aka zartar a ƙarƙashin wannan yanayi, ana iya ɗaukarta sabawa tsarin mulki.

 

Daga Aminu Dalhatu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Majalisar Dokoki Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Kasa Ta Rasha Ta Amince Da Yarjeniyar Dangantaka Ta Musamman Tsakanin Iran Da Kasar

Majalisar kasa ta kasar Rasha ta amince da yarjeniyar dangantaka ta musamman tsakanin kasar da JMI a ranar 8 ga watan Afrilun da muke ciki sannan ana saran shugaban kasa Vladimir Putin zai sanyawa yarjeniyar hannu a nan gaba.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa yarjeniyar ta musamman mai kuma dogon zango na shekaru 20 zai bawa kasashen biyu damar tallafawa juna da kuma aiki tare da bangarori daban-daban wadanda suka hada da tsaro makamashi kimiyya da fasaha da sauransu.

Labarin ya kara da cewa idan yarjeniyar ya fara aiki kasashen biyu suna da damar kyautata dangantaka a tsakaninsu, wanda zai rage dogaro da suke yi da kasashen yamma a bangarori da dama.

Dangantakar Tehran da Mosco tana kara karfi ne a dai dai lokacinda al-amuran tsaro suke kara tabarbarewa a yanking abas ta tsakiya. Har’ila yau a dai dai lokacinda kasashen biyu suke fama da takunkuman tattalin arziki mafi muni daga kasashen yamma saboda yaki tsakanin Rasha da Ukraine da kuma shirin makamashin nukliya na kasar Iran da kuma siyasarta a kudancin Asiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Kasa Ta Rasha Ta Amince Da Yarjeniyar Dangantaka Ta Musamman Tsakanin Iran Da Kasar
  • Majalisar Dokokin Zamfara Ta Dawo da Dan Majalisa Basko da Aka Dakatar
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Taron Ƙarawa Ma’aikatan Jinƙai Sani A Jihar Kano
  • Zargin Ganduje: Za mu sanar da lokacin yanke hukunci —Kotu
  • Majalisa ta gayyaci Kantoman Ribas, Ibok-Ete Ibas
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bukaci Jami’an Tsaro Mata Su Rika Sanya Hijabi Yayin Aiki
  • An Yanke Masa Hukuncin Ɗaurin shekaru 2 A Gidan Yari Saboda Yunƙurin Daɓa Wa Mahaifinsa Almakashi A Kano
  • Majalisar Kaduna ta Amince da Kudirin Kula da Lafiyar Kwakwalwa na Jihar
  • HOTUNA: Zulum ya karɓi baƙuncin Majalisar Sarakunan Arewa a Borno
  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa