An yi zanga-zangar kisan ɗalibi a Jami’ar FUDMA da ke Katsina
Published: 24th, February 2025 GMT
A wannan Litinin ɗin ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Dutsinma FUDMA suka shiga rana ta biyu ta zanga-zangar kisan wani ɗalibi da ake zargin jami’an bijilanti na JTF sun yi a ranar Lahadi.
Aminiya ta samu rahoton cewa ’yan bijilantin sun buɗe wa wasu ɗalibai da ke tafe kan babur wuta ba tare da sun tsayar da su domin tuhuma bisa zargin cewa masu yi wa ’yan bindigar daji leƙen asiri ne.
Wannan harbin da suka yi ya yi sanadiyar mutuwar wannan ɗalibi mai suna Saidu Abdulkadir.
Ana iya tuna cewa, a kwanakin baya an kama wani ɗalibin jami’ar yana safarar makamai.
Bayanai sun ce hakan ne ya sanya wasu ke tunanin ’yan bijilantin sun yi amfani da wancan lamari da ya faru har suka aikata abin da ya yi sanadiyar mutuwar wannan ɗalibi a yanzu.
Dangane da hakan ne ɗaliban ke zanga-zangar neman a gudanar da bincike tare gurfanar da waɗanda suka yi wannan kisa hukuncin da ya dace don tabbatar da adalci.
Kakakin rundunar ’yan sandan Katsina, DSP Abubakar Sadiq Aliyu ya tabbatar da faruwar hakan kuma ya ce suna kan binciken lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗalibi Jami ar FUDMA Jihar Katsina zanga zangar
এছাড়াও পড়ুন:
Ana zargin malami da azabtar da ɗalibi saboda shan mangwaro a makaranta
Ana zargin malamin makarantar Aliyu Mustapha Academy da ke Jimeta a Jihar Adamawa kan wuce gona da iri da kuma azabtar da wani ɗalibinsa a dalilin shan mangwaro a lokacin ‘break’ a harabar makarantar.
Aminiya ta ruwaito cewa a lokacin da ake tsaka da hutun tara ne malamin yan kama ɗalibin yana shan mangwaro, inda ya lakaɗa wa ɗalibin dukan tsiya.
Shaidu sun ce har da naushi malamin ya riƙa yi wa ɗalibin, lamarin da ya sa taron ya ƙuƙƙuje tare da barin sa da tabbai a jikinsa.
Malamin yana tsaka da dukan ɗalibin ne mahaifin yaron ya je makarantar domin tabbatar da biyan kudin makarantar ɗan nasa.
NAJERIYA A YAU: Matakan Kariya Daga Cutar Ƙyandar Biri Har yanzu Najeriya na buƙatar shugabanni nagari – Sheikh GumiGanin halin da ya iske ɗan nasa a sai ya sanya baki, amma malamin bai dakata ba da naushin yaron.
Mahaifin mai suna Bashiru Haman, ya ce, “Na kaɗu da ganin ana dukan yaron haka, na yi ƙoƙarin in ƙwace shi amma malamin ya ƙi barin sa. Daga nan sai an kai ƙara wajen shugabar makarantar, Misis Amanda Pam, Amma sai ta umarce ni da in fice daga harabar makarantar.”
Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Adamawa, A’isha Yanar ta tabbatar da faruwar lamarin. Ta ce, “ma’aikatar ta samu wasikar ƙorafin mahaifin ɗalibin kuma ta fara gudanar da bincike domin daukar matakin da ya dace. Za kuma mu ɗauki matakan da suka kamata domin hana faruwar irin haka a nan gaba.”
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Adamawa ta ce ta fara gudanar da bincike kan lamarin, kamar yadda kakakinta, Dankombo Morris, ya sanar.
Ya ce, “muna kira da duk masu wani bayani game da abinda ya faru da su taimaka mana da bayanai a wannan bincike da muke gudanarwa.”
A halin yanzu dai yaron mai suna Jaafar yana fama da jinya a yayin da iyayensa suke neman a ƙwato masa haƙƙi kan azabtarwar da aka yi masa.