An yi zanga-zangar kisan ɗalibi a Jami’ar FUDMA da ke Katsina
Published: 24th, February 2025 GMT
A wannan Litinin ɗin ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Dutsinma FUDMA suka shiga rana ta biyu ta zanga-zangar kisan wani ɗalibi da ake zargin jami’an bijilanti na JTF sun yi a ranar Lahadi.
Aminiya ta samu rahoton cewa ’yan bijilantin sun buɗe wa wasu ɗalibai da ke tafe kan babur wuta ba tare da sun tsayar da su domin tuhuma bisa zargin cewa masu yi wa ’yan bindigar daji leƙen asiri ne.
Wannan harbin da suka yi ya yi sanadiyar mutuwar wannan ɗalibi mai suna Saidu Abdulkadir.
Ana iya tuna cewa, a kwanakin baya an kama wani ɗalibin jami’ar yana safarar makamai.
Bayanai sun ce hakan ne ya sanya wasu ke tunanin ’yan bijilantin sun yi amfani da wancan lamari da ya faru har suka aikata abin da ya yi sanadiyar mutuwar wannan ɗalibi a yanzu.
Dangane da hakan ne ɗaliban ke zanga-zangar neman a gudanar da bincike tare gurfanar da waɗanda suka yi wannan kisa hukuncin da ya dace don tabbatar da adalci.
Kakakin rundunar ’yan sandan Katsina, DSP Abubakar Sadiq Aliyu ya tabbatar da faruwar hakan kuma ya ce suna kan binciken lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗalibi Jami ar FUDMA Jihar Katsina zanga zangar
এছাড়াও পড়ুন:
Aljeriya Ta Kori Jami’an Diflomasiyya Faransa 12
Gwamnatin kasar Ajeriya ta bayyana jami’an diflomasiyyar Faransa da suke kasar su 12 a matsayin ‘wadanda ba a bukatar ganinsu” a cikin kasar, tare da yin kira a gare su da su fice a cikin sa’oi 48.
Bugu da kari kasar ta Aljeriya ta yi suka da kakkausar murya akan ministan harkokin wajen Faransa Bruno Rotayo,tare da cewa za ta mayar masa da martanin da ya dace.
Sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Aljeriya ta bayyana cewa; A matsayinta na kasa mai cikakken shugabanci, tana daukar ma’aikatan ofishin jakadanci Faransa 12 a matsayin wadanda ba a maraba da su, sannan kuma ana bukatar da su fice daga kasar a cikin sa’oi 48.”
Aljeriya din ta dauki wannan matakin ne a matsayin mayar da martani ga kama wani jami’in diflomasiyyarta da aka yi a kasar Faransa a ranar 8 ga watan Aprilu da ake ciki.
Aljeriyan ta bayyana abinda ya faru da cewa, keta hurumin kasarta ne da kuma take dokokin aikin diflomasiyya.”
Haka nan kuma ta yi ishar da cewa, ma’aikacin diflomasiyyar da aka kama yana da kariya ta aiki wacce ta hana a yi masa abinda ya faru,amma kuma gwamnatin Faransa ta yi mu’amala a shi ta hanya mafi muni da halayya irin ta barayi.’
Alaka a tsakanin Faransa da Aljeriya tana kwan-gaba da baya, musamman a cikin watannin bayan nan. Watanni 8 da su ka gabata an sami rashin jituwa a tsakaninsu saboda korar wasu ‘yan asalin Aljeriya mazauna Faransa bisa zargin cewa sun shiga kasar ba bisa ka’ida ba. Aljeriya ta yi wa jakadanta kiranye, tare da rufe kafar diflomasiyya a tsakaninsu na tsawon watanni 8.