Hukumar Tsaro Ta Farin Kaya Ta Kama Wasu Mutane 2 Da Yin Sojan Gona
Published: 24th, February 2025 GMT
Hukumar tsaro ta farin kaya (NSCDC) reshen jihar Kano ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da yin sojan gona ga aikin hukumar.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar NSCDC reshen jihar Kano SC Ibrahim Idris Abdullahi ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano.
Ya ce mutanen biyu, Muhammad Sarari da Madaki Zaharaddeen, masu shekaru 43 da 32, mazauna Goron Dutse ne, a karamar hukumar Dala, da Hotoro kwatas a karamar hukumar Nassarawa.
A cewar jami’in hulda da jama’an, wadanda ake zargin suna zuwa hukumomin da ma’aikatun gwamnati ne, inda suke yaudarar manyan ma’aikata tare karbar kudade daga hannunsu.
“Dubunsu ta cika ne a lokacin da suka yi yunkurin tsoratar da wasu manyan ma’aikatan gidan talabijin na jihar, suna neman su basu wasu kudade.” In ji shi.
Jami’an hukumar ta NSCDC reshen Tarauni ne suka kama wadanda ake zargin, inda aka kawo su hedikwatar jihar domin yi musu tambayoyi.
Da aka gudanar da bincike, sun amince da aikata laifin, kuma an sami daya daga cikinsu da katin shaida na bogi da rigar ciki mai dauke da tambarin hukumar NSCDC.
Ya kuma yi nuni da cewa, za a tuhumi wadanda ake zargin ne da laifin shiga harkar aikin gwamnati, da hada baki, da tsoratarwa, da kuma karbar kudi.
Abdullahi ya kara da cewa hukumar NSCDC reshen jihar Kano ta kammala bincikenta, za kuma kuma a kaisu gaban kotu.
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar NPC Za Ta Gudanar Da Kidayar Jama’a Cikin Aminci- Shugaba Tinubu
Shugaba Bola Tinubu ya ce Najeriya ta dauki wani muhimmin mataki na gudanar da kidayar jama’a da gidaje da aka jima ba a yi ba, inda ya tabbatar da cewa za a gudanar da aikin cikin inganci ta hanyar amfani da fasahar zamani.
Shugaban ya ba da wannan tabbacin ne a wata ganawa da ya yi da jami’an hukumar kula da yawan jama’a ta kasa (NPC) a fadar gwamnati, shugaba Tinubu ya jaddada muhimmancin kidayar jama’a ga tsare-tsare na kasa, tare da jaddada aniyarsa na tabbatar da tattara bayanai masu inganci.
Shugaba Tinubu ya bayyana shirin kafa kwamitin da zai duba kasafin kidayar jama’a da kuma gano hanyoyin samun kudade.
Ya kuma jaddada bukatar hukumar kula da tantance ‘yan kasa (NIMC) ta taka rawar gani wajen gudanar da wannan aiki, tare da tabbatar da samar da ingantattun na’urorin tantancewa da suka hada da tantance fuska da murya.
Shugaban ya bayyana cewa ingantattun bayanan za su haɓaka shirye-shiryen gwamnati, musamman a fannin aikin gona da walwalar jama’a.
Ministan Kasafin Kudi da Tsare Tattalin Arziki, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, ya tabbatar da kudurin na Tinubu, inda ya bayyana cewa rashin kudi ne ya janyo tsaikon kidayar jama’a.
Ya kuma bayyana cewa, NPC ta riga ta kammala muhimman ayyukan shirye-shirye da suka hada da kidayar jama’a, sannan kuma hukumomin tantancewa da kididdiga daban-daban kamar su NPC, NIMC, NBS, da Ma’aikatar Tattalin Arziki, suna aiki tare don inganta bayanan da ake da su.
Daga Bello Wakili