Hukumar tsaro ta farin kaya  (NSCDC) reshen jihar Kano ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da yin sojan gona ga aikin hukumar.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar NSCDC reshen jihar Kano SC Ibrahim Idris Abdullahi ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano.

Ya ce mutanen biyu, Muhammad Sarari da Madaki Zaharaddeen,   masu shekaru 43 da 32, mazauna Goron Dutse ne, a karamar hukumar Dala, da Hotoro kwatas a karamar hukumar Nassarawa.

A cewar jami’in hulda da jama’an, wadanda ake zargin suna zuwa hukumomin da ma’aikatun gwamnati ne, inda suke yaudarar manyan ma’aikata tare karbar kudade daga hannunsu.

“Dubunsu ta cika ne a lokacin da suka yi yunkurin tsoratar da wasu manyan ma’aikatan gidan talabijin na jihar, suna neman su basu wasu kudade.” In ji shi.

Jami’an hukumar ta NSCDC reshen Tarauni ne suka kama wadanda ake zargin, inda aka kawo su hedikwatar jihar domin yi musu tambayoyi.

Da aka gudanar da bincike, sun amince da aikata laifin, kuma an sami daya daga cikinsu da katin shaida na bogi da rigar ciki mai dauke da tambarin hukumar NSCDC.

Ya kuma yi nuni da cewa, za a tuhumi wadanda ake zargin ne da laifin shiga harkar aikin gwamnati, da hada baki, da tsoratarwa, da kuma karbar kudi.

Abdullahi ya kara da cewa hukumar NSCDC reshen jihar Kano ta kammala bincikenta, za kuma kuma a kaisu gaban kotu.

 

Abdullahi Jalaluddeen

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdullahi Usman, ya rasu

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Taraba, SP Abdulahi Usman, ya rasu bayan fama da doguwar jinya.

Kakakin rundunar ’yan sandan Najeriya, Olumuyiwa Adejobi ne, ya tabbatar da rasuwarsa cikin wata sanarwa a ranar Laraba.

’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa Ribas: Za mu ɗauki matakan da za su shafi tattalin arzikin Nijeriya — ’Yan ƙwadago

Ya bayyana Usman a matsayin jajirtaccen ɗan sanda kuma gada tsakanin jami’an tsaro da al’umma.

“SP Usman ya shafe shekaru uku yana ƙarfafa hulɗa tsakanin ’yan sanda da jama’ar Taraba.

“Ƙwarewarsa, mutuntaka da jajircewarsa wajen neman adalci sun an samu tasiri,” in ji Adejobi.

Ya ƙara da cewa rasuwar Usman babban rashi ne ga rundunar ’yan sanda, abokan aikinsa da duk wanda ya san shi.

Sashen hulɗa da jama’a na ’yan sanda ya miƙa ta’aziyya ga iyalansa da kuma ‘yan uwansa, tare da yin addu’ar Allah Ya masa rahama.

Za a ci gaba da tunawa da Usman saboda sadaukarwar a aikinsa da ƙoƙarinsa na kyautata hulɗa tsakanin ’yan sanda da al’umma a Jihar Taraba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ahmad Lawan ya raba tallafin N27m da buhun shinkafa 300 a Yobe
  • Hadimin Gwamnan Kano, Abdullahi Tanka, Ya Rasu
  •  Nigeria: An  Kashe Sojoji Da DAma A Wani Hari Da Aka Kai Wa Sansanonin Soja Biyu Hari A Jihar Borno
  • Jagoran Juyin Musulunci Ya Amince Da Yin Afuwa Ga Wasu Fursunoni Masu Yawa
  • Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdullahi Usman, ya rasu
  • ’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa
  • Gwamnatin Kano za ta hukunta masu shigar banza a bikin Sallah
  • Hukumar IAEA ta yi ishara da yiwuwar sake komawa teburin tattaunawa tare da Iran
  • NIDCOM: An Ceto ‘Yan Nijeriya Sama Da 950 Daga Gidajen Kurkuku A Libya
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Kafa Rundunar Daukin Gaggawa Don Magance Matsalolin Tsaro