Leadership News Hausa:
2025-03-28@03:52:56 GMT

Ministan Gidaje, Ba Ɗan Jam’iyyar APC Ba Ne – Shugaban APC Na Kano

Published: 24th, February 2025 GMT

Ministan Gidaje, Ba Ɗan Jam’iyyar APC Ba Ne – Shugaban APC Na Kano

Ministan ya yi zargin cewa, furucin Shugaban na daya daga cikin dalilan da suka sa Allah ya karbe mulki daga jam’iyyar duk da nasarar da ta samu a zaben gwamna na 2023.

 

Amma da yake mayar da martani, Abbas ya yi zargin cewa Ata ya yi wa jam’iyyar zagon kasa a zaben 2023, kuma sun bayyana haka ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

 

Abdullahi Abbas ya ce, “A gare mu ‘yan APC Yusuf Ata ba dan jam’iyyar APC ba ne. Ba mu ma san dalilin da ya sa aka nada shi minista ba. Duk fadin jihar Kano a karamar hukumarsa ne muka zo na uku a zaben 2023.

 

“Ba mu san cewa an nada shi minista ba. Mun gaya wa shugaban kasa cewa shi ba dan jam’iyyarmu ba ne. Ya yi wa jam’iyyar zagon kasa.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan tsaro ya yi alƙawarin kawo sauyi a cibiyar horar da sojoji

Ministan Tsaro, Mohammed Abubakar Badaru, ya ziyarci Cibiyar Horar da Sojoji da ke Zariya, inda ya yi alƙawarin samar da ƙarin kayan aiki da ci gaba da inganta horon kuratan sojoji domin su dace da buƙatun zamani.

A lokacin ziyarar, Ministan ya bayyana gamsuwarsa da horon da kurata na kashi 88 ke samu, inda ya jaddada aniyar Gwamnatin Tarayya na bunƙasa kayan horo da samar da ingantattun makamai da kayan aiki ga dakarun sojoji.

Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdullahi Usman, ya rasu Ban sani ba ko zan tsaya takara a 2027 — Atiku

Badaru ya yi alƙawarin tuntuɓar Gwamnatin Jihar Kaduna, domin kammala ginin Makarantar Sakandaren Chindit, wadda ba a kammala ta ba tsawon lokaci.

Ya kuma bayar da tabbacin samar wa Makarantar Firamare ta Chindit kayan aiki domin inganta ilimin ’ya’yan sojojin da ke barikin.

Baya ga haka, ministan ya amince da samar da rijiyoyin burtsatse a barikin, domin shawo kan matsalar ƙarancin ruwa da ake fuskanta a Depot Zariya.

A jawabinsa na maraba, Kwamandan Depot, Manjo Janar Ahmadu Mohammed, ya gode wa ministan bisa wannan ziyarar, tare da bayyana yadda Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ke ba su goyon baya domin magance matsalolinsu.

Ya kuma bayyana cewa za su ci gaba da samar da ƙwararrun sojoji masu kishin ƙasa da jajircewa.

Ziyarar ministan ta samu rakiyar manyan jami’an tsaro, ciki har da Babban Sakataren Ma’aikatar Tsaro, Jakada Gabriel Aduda, da Manjo Janar Ahmed Jubrin (mai ritaya), da kuma Birgediya Janar Aminu Garba.

Hakazalika, wasu manyan hafsoshin soji irin su Kwamandan Armed Forces Command and Staff College, Air Marshal Hassan Alhaji, da Kwamandan Makarantar Motsa Jiki ta Sojojin Najeriya, Birgediya Janar Owoicho Ejiga, na cikin tawagar.

Ziyarar na daga cikin ƙoƙarin ministan na ganin an inganta cibiyoyin horon sojoji domin tabbatar da nagartar jami’an tsaro a Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ina Fatan Ci Gaba Da Kasancewa A Manchester United – Onana
  • Zamu Tabbatar Ingantuwar Depon Sojoji Na Zaria – Ministan Tsaro Badaru
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata a matsayin hutun sallaGwamnati Ta Ayyana 31 Ga Maris Da 1 Ga Afrilu A Matsayin Ranakun Hutu Don Bukin Eid-el-Fitr Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 31 ga Maris, da Talata, 1 ga Afrilu, a matsayin ranakun hu
  • Wang Yi Ya Gana Da Mataimakin Shugaban Kwamitin Kasa Na Amurka Mai Lura Da Alakar Sin Da Amurka
  • Kwalara Ta Kashe Mutum 14, Ana Zargin 886 Sun Kamu A Nijeriya – NCDC
  • Ministan tsaro ya yi alƙawarin kawo sauyi a cibiyar horar da sojoji
  • Majalisa Ta Yi Watsi Da Kara Akan Akpabio Kan Zargin Neman Yin Lalata Da Natasha
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Zargin Kasar Amurkan Dangane Da Kamfanonin Man Fetur Na Kasar Ba Gaskiya Bane
  • An Ceto ‘Yan Nijeriya Sama Da 950 Daga Gidajen Yari A Libya – Gwamnati
  • SDP: Ba Mu Yi Wa Kowa Alƙawarin Takarar Shugaban Ƙasa Ba